• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Cikin Gidan APC Da PDP: Shin ‘Yan Jihar Ribas Kadai Aka Bata Wa Rai?

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rikicin Cikin Gidan APC Da PDP: Shin ‘Yan Jihar Ribas Kadai Aka Bata Wa Rai?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan muka duba rikicin cikin gida na jam’iyyun siyasa yana samun asali ne kan yadda ake tafiyar da ita siyasar a tsakanin shugabanninta. Bari mu fara da jam’iyyar APC da take rike da mulkin kasa da kuma Jihohi masu rinjaye.

Dole ne rikici ya rika tasowa lokaci zuwa lokaci wannan kuma hakane rayuwa ta gada domin ba kullum bane ake kwana gado ba.

  • PDP Ta Nada Tambuwal Daraktan Yakin Neman Zaben Atiku

Mutum ya kamata ace ya saba da hakan kamar dai yadda harshe da hakori ma watarana ana dan batawa, kuma abin ba a jin dadi ko kadan da akwai wuya. Akwai abubuwa da yawa da su kan faru a jam’iyya wadanda ba a sanin su domin ba a bari har su kai ga fitowa fili har wasu su kai ga jin irin halin da ake ciki.

Kamar dai abinda ya faru a jam’iyyar APC wanda bayan da aka yi zaben fidda gwani na jam’iyyar ne a ranar 8 ga watan Yuni 2022, cikin wannan makon ne abin boye ya fito fili, ashe an bata ma wasu rai a jam’iyyar amma suna nan ba za su fita ba, ba za su bar ta ba.

Ko shakka babu tsohon gwamnan Jihar Ribas har ila yau kuma tsohon Ministan Sufuri Chibuke Rotimi Amechi, ya b ada gaggarumar gudunmawa a jam’iyyar APC.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Tunlokacin da ya dawo jam’iyyar cikinta tare da tsohon gwmnanJihar Kwara tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki. Shi ma tsohon shugaban majalisar wakilai ta tarayyya Aminu Waziri Tambuwal tare da har ila yau tsohon mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar haka suka baro wurin da ake taron PDP suka zarce zuwa dakin taro na ‘Yar’adua Centre inda daga can suka bada labarin ficewarsu daga jam’iyyar.

Kafin ya dawo jam’iyyar APC lokacin yana PDP ba karamar gwagwarmaya ya yi da shan wahala cikin Jihar ta su ta Ribas ba, da ma sashen na Kudu maso Kudu gaba daya, amma duk da hakan ya yi hakuri da ci gaba da zama a jam’iyyar.

Lokacinzaben fidda gwani na jam’iyyar APC shi ya kasance na biyu wanda yake bin Sanata Bola Ahmed Tinubu da ya kasance dan takarar jam’iyyar, mataimakin Shugaban kasa Farfesa Osinbajo ya zama na uku.

Komai aka fada kan Amechi ba zai isa ba kan gudunmawar da yake ci gaba da ba jam’iyyar APC.Har zuwa lokacin da aka bayyana sunayen wadanda za su taimaka wajen yakin neman zabe na dan takarar jam’iyyar APC na dukkan mukaman ba a ji an ambaci sunan sa ba.

Wike kamar Amechi dan Jihar Ribas ne amma shi dan jam’iyyar PDP ne yana ta bata gudunmawa wajen tafiyar da ita, domin ba gamawa ya yi ba.

Idan dai jama’a ba mantawa suka yi ba lokacin da jam’iyyar ta shiga cikin babban rikicin Shugabancinta daga karshe sai da Uche Sokondus Shugaban jam’iyyar na lokacin ya sauka.

Bayan an yi zaben da ya samar da Sanata Iyorchia Ayu a matsayin Shugaban jam’iyyar, sai bayan da aka yi zaben fidda gwani ne na jam’iyyar PDP. Tsohon mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar ya zama dantakarar Shugaban kasa na jam’iyyar.

Kamar dai yadda aka saba sai abin ya zama kamar ‘yan tagwaye shi ma Wike ya zo na biyu kamar dai Amechi shi ma haka ya kasance sai ba a jawo shi a jiki ba. Maimakon haka ma sai aka mai da shi saniyar ware, kamar dai yadda aka yi ma tsohon Ministan Sufuri Chibuke Rotimi Amechi aka mai da Garma da aka shekara aiki da ita amma aka barta tsirara.

Tun lokacin da aka kammala zaben fidda gwani na jam’iyyar, ba a faye jin duriyarsa ba,bai yin magana kan wani al’amari shi ma, ba,a yin maganar data shafe shi.

Irin hakan ne ya sa yanzu ya zame masu Kadangaren bakin Tulu a kashe shi a kar Tulun idan kuma aka bar shi ya bata ruwan.Ya tada ma jam’iyyar hankali har zuwa yanzu abubuwa a kudundune suke suna tafiyar Hawainiya, domin kuwa bayan kwamitocin da aka kafa biyu sun kasa zama.

Dagakarshe ma har Atiku da Wike suka hadu a London suka yi kwalli da juna amma abin har yanzu da sauran rina a Kaba.Shi ma bai ce zai bar jam’iyyar ba,sai dai ya yi mata wani jirwaye mai kamar wanka inda yace zai taimaka mata ta fadi zabe.

Matsawa da maganganun da Wike ya ci gaba da yi ta sa har Shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar Sanata Wali Jibril ya sauka daga kan mukaminsa.Amma har yanzu Wike bai amince da hakan ba so yake Ayu ya sauka daga jagorancin jam’iyyar gaba daya, watakila idan da an ba shi mataimakin dantakarar Shugaban kasa na jam’iyyar da tuni an wuce wurin da ake yanzu.
Amma babu wani abu kwakkwara da aka yi ma shi watakila shi yasa har yanzu hankalinsa ba kwanciya ya yi ba, me yiyuwa ne har sai lokacin da yaga Ayu ya yada kwallon Mangwaro domin ya huta da Kuda.
Ba Amechi da Wike kadai ba ne aka taba bata ma rai a siyasance ba idan aka yi la’akari da yadda siyasar take tafiya halin da ake ciki yanzu, sai dai mutanen biyu wadanda ana iya cewa sun zama tamkar tagwaye ne a wasu abubuwa sun dai dan bambanta ne. Suna cikin shan gwagwarmayar siyasa domin ai ba gamawa suka yi ba, suna yi ma siyasar aiki tukuru matuka sai dai har yanzu hakarsu bata kai ga cimma ruwa ba tukunna.
Amechi ya bar jam’iyyar PDP ya koma ta APC sai dai shi kuma Wike har yanzu yana nan a PDP bai taba barinta ya koma ma wata jam’iyya ba. An kuma san gwarzon yin ayyukan ci gaban al’ummar shi ne.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Daukakar Nasaba Da Girman Garin Annabi Muhammadu (SAW)

Next Post

Kwalara Ta Mamaye Sansanin Tubabbun ‘Yan Boko Haram, 2 Sun Mutu A Cikinsu A Borno

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Kwalara Ta Mamaye Sansanin Tubabbun ‘Yan Boko Haram, 2 Sun Mutu A Cikinsu A Borno

Kwalara Ta Mamaye Sansanin Tubabbun 'Yan Boko Haram, 2 Sun Mutu A Cikinsu A Borno

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.