• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Falasdinawa Da Isra’ila Na Kara Rincabewa

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Falasdinawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A karo na farko Hamas ta harba makamai masu linzami kan filin jirgin sama na ‘Ben Gurion airport’ da ke birnin Tel Avib babban birnin kasa Isra’la.

A birnin San Francisco na Amurka kuwa dubban mutane suka yi zanga zangar goyon bayan Falasdinawa, da kuma la’antar Israila.
Kawo yanzu yahudawa 2,382 suna kwance hajaran majaran cikin munanan raunuka, wasu na ma na iya mutuwa a koda yaushe.
Israila ta sanar da cewar an sake kashe mata sojoji 16 a bakin daga, amma kafofin Falastinawa sun bayyana cewar lamarin ya linka hakan sosai.

  • Kungiyar Kasashen Larabawa Ta Yi Taro Kan Rikicin Isra’ila da Falasdinu
  • Rikicin Falasdinu Da Isra’ila: Saudiyya Ta Dakatar Da Duk Wata Tattaunawa Da Isra’ila

Israila ta sanar da cewar yahudawan da suka mutu sun kai mutun 1,030. Anadolu News Agency sun tabbatar da hakan.

Kafofin sadarwar Israila sun bayyana cewar yahudawan da ke Hannun Hamas sun kai mutum 150. Hamas ta ce cikinsu mutum 100 duk sojoji ne har da manyan jami’an sojan yahudu.

Hukumomin lafiya a Falastinu sun sanar da cewar Falastinawa 456 suka yi shahda, a cikinsu akwai yara 78 sai mata 46. Tashar Aljazeera ta tabbatar da hakan.

Labarai Masu Nasaba

An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila

Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

Shugaban kungiyar HAMAS Ismail Abu Haniye ya tattauna da shugaban kasar Iran, ya yi masa karin haske kan halin ďa ake ciki. Ya yi wa shugaban da kuma al’ummar Iran godiya bisa gòyon bayan da suke bai wa Falastinawa.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi zaman sirri kan yakin amma har yanzu sun kasa cimma matsaya daya, ana sa ran za su ci gaba da zaman domin ganin abin da zai yiwu.

Bayanai sun nuna cewa, adadin mamata na karuwa a tsakanin dakarun Hamas da na Isra’ila a Gaza, Isra’ila ta sake karbe iko da yankunan kan iyakar Zirin Gaza, a yayin da adadin wadanda suka mutu a bangarorin biyu ke ci gaba da karuwa, sakamakon rikicin da ya barke, biyo bayan wani mummunan harin da kungiyar Hamas ta kaddamar kan yankunan da Israila ta mamaye , wanda ba a taba ganin irinsa ba.

A yayin da Isra’ila ta zafafa hare-haren sojinta kan yankin Zirin Gaza, an jiyo wani kakakin ma’aikatar tsaron kasar, Laftanar Kanar Jonathan Conricus na cewa, yawan adadin rayukan mutanen da suka salwanta a bangaren Yahudawan ya kai dubu 1.200
Ya ce Isra’ila ta jibge dakaru dubu dari 300 a kusa da yankin Zirin Gaza, wadanda ke a shirye don aiwatar da umurnin da gwamnatin kasar ta ba su.

A bangaren Falasdinawa kuma, ma’aikatar kiyon lafiyar yankin Zirin Gaza ta ce, adadin wadanda suka mutu ya haura mutane dari 900, a yayin da hare-haren da Isra’ila ke kai wa yankin ke ci ga da kamari.

Kamfanin da ke samar da wutar lantarki a yankin na Gaza da ke kunshe da yawan al’umma sama da miliyan 2, ya ce, wutar lantarki na iya daukewa nan da ‘yan sa’o’i, sakamakon karancin makamashin da tashar samar da wutar fama dashi.

Zirin-Gaza ya yi ta fama da daukewar wutar lantarki tun bayan harin da kungiyar HAMAS ta kai cikin yankunan da Isra’ila ta mamaye, sakamakon luguden wuta da dakarun na Isra’ila su ke ta yi babu kakkautawa kan yankin na Gaza tun safiyar ranar Asabar da ta gabata, abin da ya sa hatta asibitoci a mafi yawan lokuta, ke gudanar da ayuka cikin duhu ba tare da wutar lantarki ba.

Kasashe da al’ummar duniya suna ta kiraye-kiraye ga bangarorin biyu da su kai zuciya nesa su stakaita wuta don rage kuncin da al’umma suka shiga a yankunan biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinawaGazaHamasIsra'ilawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsoron Allah Da Ibadar Annabi (SAW)

Next Post

Daliban Nijeriya 99,985 Suka Arce Zuwa Jami’o’in Ingila Cikin Shekara 5  — Minista

Related

Noma
Labarai

An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila

54 minutes ago
Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato
Labarai

Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

1 hour ago
Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba
Labarai

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

2 hours ago
uba sani
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

3 hours ago
Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu
Labarai

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

5 hours ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

5 hours ago
Next Post
Daliban Nijeriya

Daliban Nijeriya 99,985 Suka Arce Zuwa Jami’o’in Ingila Cikin Shekara 5  — Minista

LABARAI MASU NASABA

Noma

An Shiga Damuwa Yayin Da Gwamnatin Nijeriya Ke Jinkiri Wajen Biyan ‘Yan Kwangila

September 5, 2025
Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

Sojoji Sun Cafke Ɗan Ta’adda Ɗauke Da Makamai A Filato

September 5, 2025
Ministan Wajen Najeriya: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Samarwa Afirka Damammakin Ci Gaba

Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Nijeriya Sun Koka Kan Rashin Biyan Basussukan Albashi

September 5, 2025
uba sani

Gwamnatin Kaduna Ta Zargi El-Rufai Da Yunkurin Tayar Da Tarzoma A Jihar

September 5, 2025
Manzon Allah

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

September 5, 2025
Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

September 5, 2025
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Ministan Tsaro

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

September 5, 2025
Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.