ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Masarautar Kano: Lauyoyi Da Alƙalai Sun Tozarta Ɓangaren Shari’a – Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi

by Sulaiman
2 years ago
Kano

Shugaban kungiyar lauyoyin Nijeriya (NBA), Yakubu Maikyau, ya koka kan rawar da wasu lauyoyi da kotuna suka taka a kan hukunce-hukunce masu cin karo da juna dangane da rikicin masarautar Kano.

Wasu kotuna biyu a jihar Kano sun fitar da wasu umarnin wucin gadi masu cin karo da juna kan rikicin masarautar Kano.

  • Majalisar Wakilai Za Ta Binciki CBN Kan Korar Ma’aikata 600
  • Dattawan Kudancin Kano 103 Sun Buƙaci Gwamna Abba Ya Dawo Da Sarakuna 5 Da Aka Rushe

Mai shari’a S. A. Amobeda na babbar kotun tarayya da ke Kano a ranar Talata ya bayar da umarnin korar mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II daga fadar Gidan Rumfa.

ADVERTISEMENT

Sai dai mai shari’a Amina Adamu Aliyu ta Babbar Kotun Jihar Kano ta bayar da wani umarni na daban, inda ta haramtawa ‘yansanda, hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da kuma rundunar sojojin Nijeriya daga korar Sanusi, ko muzgunawa ko kamawa.

Sarki Sanusi da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, na fafatawa da juna domin neman kujerar sarauta. Rikicin dai ya janyo zanga-zangar magoya bayan kowanne bangare a Kano.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Da yake mayar da martani kan lamarin, Babban lauyan Nijeriya (SAN), Maikyau a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba,  Daily Trust ta rahoto ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda lauyoyi da alkalan da ke da hannu a cikin shari’ar ke gudanar da ayyukansu.

Ya yi nuni da cewa, akwai bukatar a sake yin nazari cikin gaggawa kan yadda kwararrun lauyoyi da alkalan da ke da ruwa da tsaki a wadannan al’amura ke gudanar da ayyukansu.

Shugaban NBA ya yi kira ga shugabannin kotunan da su binciki yadda alkalan ke gudanar da ayyukansu tare da kai rahoton bincikensu ga hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa (NJC) domin daukar matakin da ya dace.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Li Qiang Ya Yi Kira Ga Sin Da Equatorial Guinea Da Su Kare Moriyar Bai Daya Ta Kasashe Masu Tasowa

Li Qiang Ya Yi Kira Ga Sin Da Equatorial Guinea Da Su Kare Moriyar Bai Daya Ta Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.