• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Uba Sani Da El-Rufa’i Ya Dauki Sabon Salo

byRabi'u Ali Indabawa
8 months ago
Uba sani

Rikicin da ake tsakanin tsohon gwamnan Jihar Kaduna da gwamna mai ci Uba Sani na ci gaba da daukar sabon salo, inda dukkaninsu ke kai wa juna hare-hare cikin kalamai.

Gwamna Sani a wata hira da ya yi a gidan talabijin na kasa ranar Litinin ya yi kakkausan suka ga abin da ya kira gamayyar ‘yan siyasa da suka taru kwanan nan don sukar gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Mutum 2, Sun Yi Garkuwa Da Wasu 5 A Kaduna.
  • Zanga-zanga: Ku Kawo Ƙarshen Rashin Wutar Lantarki Da Ta Addabi Jihohi- Gwamnatin Kaduna 

A cikin hirar, gwamnan ya zarge su da adawa da gwamnati don neman mulki kawai maimakon samar da ingantattun hanyoyin magance kalubalen da ke addabar Nijeriya.

Gwamnan ya bayyana cewa babu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar da zai iya adawa da manufofin dimokuradiyyar Tinubu, yana mai jaddada cewa shugaban ya yi gwagwarmaya kuma ya tsaya tsayin daka wajen tabbatar da dimokradiyya.

Idan dai ba a manta ba a makon da ya gabata ne Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, tsohon gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, na cikin wasu manyan ‘yan siyasa da suka hallara a wani taro a Abuja, inda suka caccaki gwamnatin Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC mai mulki.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Gwamna Sani ya bayyana zargin da kungiyar ta yi a matsayin maras tushe, yana mai jaddada cewa “Mafi yawan ‘yan siyasar da ke irin wadannan kalamai na iya zama suna magana da kansu ne kawai,” in ji shi. “Mun kasance a cikin jam’iyya daya a wani lokaci, kuma dole ne in ce na yi mamakin abin da suka yi.”

Ya kara da cewa kawancen ba shi da wata hujjoji ta gaskiya kan ikirarin nasu.

“Fito da zarge-zarge ba tare da hujja ba, wani yunkuri ne kawai na kawar da hankulan ‘yan Nijeriya,” in ji gwamnan.

“Yawancin wadannan ‘yan siyasa sun rike mukamai a gwamnati kasa da shekaru biyu da suka gabata. Me suka yi a lokacin da suke kan mulki?”

Ya nuna shakku kan sahihancinsu, yana mai nuni da cewa yakinsu sun yi ne kawai a lokacin suna kan mulki.

“Yan Najeriya suna fa fahimta, kuma sun riga sun san wadannan ’yan siyasa ba wai suna fada da Tinubu ba ne saboda sun fi shi sanin abin da ya fi dacewa da su, a’a sun samu dama a baya amma me suka yi?

Gwamna Sani ya kara da cewa a kwanakin baya wasu ‘yan siyasa sun yaba wa Shugaba Tinubu amma sun canja ra’ayinsu bayan barin gwamnati.

“Mafi yawansu suna zaune a teburi daya da mu, suna yakar Tinubu saboda mun yi imanin cewa shi ne mutumin da ya fi dacewa ya ciyar da kasar nan gaba,” in ji shi. “Mene ne shaidar dimokuradiyya, idan zan iya tambaya? Me suka yi domin ciyar da dimokuradiyya gaba a Nijeriya?” Ya tambaya.

A martanin da El-Rufai ya mayar a shafinsa na D, ya caccaki gwamnan, yana mai cewa, “Mutanen Jihar Kaduna za su yi hukunci.”

El-Rufai, a cikin shafinsa na D mai taken “Kaduna Update,” ya ce gwamnan yana “borin kunya ne da rudani” a kowace rana.

“Ina mamakin dalili, ko da yake na tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ‘ramawa’ kura aniyarta, ya bai wa Kaduna tallafin da ya haura Naira biliyan 150, a cikin watanni 18 da suka gabata, yanzu ya bayyana komai.”

“Ta kowane hali suke kare Asiwaju don samun kudi bisa sharadi. Asiwaju ya amfana da ku. Al’ummar Jihar Kaduna za su yi hukunci a daidai lokacin da ya dace, kamar yadda ya rubuta.

A wani labarin kuma, El-Rufai ya ruwaito cewa, tsohon firaministan kasar Birtaniya Tony Blair na cewa a wani lokaci da ya gabata: “ Cikin kasashe masu tasowa, inda mutane ke gwagwarmayar sanya abin da za su sa a bakinsu, zuwa makaranta, samun ilimin kiwon lafiya na yau da kullum, samar da rayuwa ba sana’a ba, (ayyukan zamantakewa) bayarwa na iya zama bambanci tsakanin rayuwa da mutuwa; ko akalla bambanci tsakanin rayuwa mai cike da bege da wacce ta sava da hakan.

“Su (‘yan kasa) suna son a magance matsalolin da ke shafar rayuwarsu ko a rage su. Suna son ingantacciyar rayuwa, ingantaccen kiwon lafiya, ilimi da tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version