ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Uba Sani Da El-Rufa’i Ya Dauki Sabon Salo

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Uba sani

Rikicin da ake tsakanin tsohon gwamnan Jihar Kaduna da gwamna mai ci Uba Sani na ci gaba da daukar sabon salo, inda dukkaninsu ke kai wa juna hare-hare cikin kalamai.

Gwamna Sani a wata hira da ya yi a gidan talabijin na kasa ranar Litinin ya yi kakkausan suka ga abin da ya kira gamayyar ‘yan siyasa da suka taru kwanan nan don sukar gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

  • ‘Yan Bindiga Sun Harbe Mutum 2, Sun Yi Garkuwa Da Wasu 5 A Kaduna.
  • Zanga-zanga: Ku Kawo Ƙarshen Rashin Wutar Lantarki Da Ta Addabi Jihohi- Gwamnatin Kaduna 

A cikin hirar, gwamnan ya zarge su da adawa da gwamnati don neman mulki kawai maimakon samar da ingantattun hanyoyin magance kalubalen da ke addabar Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya bayyana cewa babu daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar da zai iya adawa da manufofin dimokuradiyyar Tinubu, yana mai jaddada cewa shugaban ya yi gwagwarmaya kuma ya tsaya tsayin daka wajen tabbatar da dimokradiyya.

Idan dai ba a manta ba a makon da ya gabata ne Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, tsohon gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, na cikin wasu manyan ‘yan siyasa da suka hallara a wani taro a Abuja, inda suka caccaki gwamnatin Shugaba Tinubu da jam’iyyar APC mai mulki.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Gwamna Sani ya bayyana zargin da kungiyar ta yi a matsayin maras tushe, yana mai jaddada cewa “Mafi yawan ‘yan siyasar da ke irin wadannan kalamai na iya zama suna magana da kansu ne kawai,” in ji shi. “Mun kasance a cikin jam’iyya daya a wani lokaci, kuma dole ne in ce na yi mamakin abin da suka yi.”

Ya kara da cewa kawancen ba shi da wata hujjoji ta gaskiya kan ikirarin nasu.

“Fito da zarge-zarge ba tare da hujja ba, wani yunkuri ne kawai na kawar da hankulan ‘yan Nijeriya,” in ji gwamnan.

“Yawancin wadannan ‘yan siyasa sun rike mukamai a gwamnati kasa da shekaru biyu da suka gabata. Me suka yi a lokacin da suke kan mulki?”

Ya nuna shakku kan sahihancinsu, yana mai nuni da cewa yakinsu sun yi ne kawai a lokacin suna kan mulki.

“Yan Najeriya suna fa fahimta, kuma sun riga sun san wadannan ’yan siyasa ba wai suna fada da Tinubu ba ne saboda sun fi shi sanin abin da ya fi dacewa da su, a’a sun samu dama a baya amma me suka yi?

Gwamna Sani ya kara da cewa a kwanakin baya wasu ‘yan siyasa sun yaba wa Shugaba Tinubu amma sun canja ra’ayinsu bayan barin gwamnati.

“Mafi yawansu suna zaune a teburi daya da mu, suna yakar Tinubu saboda mun yi imanin cewa shi ne mutumin da ya fi dacewa ya ciyar da kasar nan gaba,” in ji shi. “Mene ne shaidar dimokuradiyya, idan zan iya tambaya? Me suka yi domin ciyar da dimokuradiyya gaba a Nijeriya?” Ya tambaya.

A martanin da El-Rufai ya mayar a shafinsa na D, ya caccaki gwamnan, yana mai cewa, “Mutanen Jihar Kaduna za su yi hukunci.”

El-Rufai, a cikin shafinsa na D mai taken “Kaduna Update,” ya ce gwamnan yana “borin kunya ne da rudani” a kowace rana.

“Ina mamakin dalili, ko da yake na tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya ‘ramawa’ kura aniyarta, ya bai wa Kaduna tallafin da ya haura Naira biliyan 150, a cikin watanni 18 da suka gabata, yanzu ya bayyana komai.”

“Ta kowane hali suke kare Asiwaju don samun kudi bisa sharadi. Asiwaju ya amfana da ku. Al’ummar Jihar Kaduna za su yi hukunci a daidai lokacin da ya dace, kamar yadda ya rubuta.

A wani labarin kuma, El-Rufai ya ruwaito cewa, tsohon firaministan kasar Birtaniya Tony Blair na cewa a wani lokaci da ya gabata: “ Cikin kasashe masu tasowa, inda mutane ke gwagwarmayar sanya abin da za su sa a bakinsu, zuwa makaranta, samun ilimin kiwon lafiya na yau da kullum, samar da rayuwa ba sana’a ba, (ayyukan zamantakewa) bayarwa na iya zama bambanci tsakanin rayuwa da mutuwa; ko akalla bambanci tsakanin rayuwa mai cike da bege da wacce ta sava da hakan.

“Su (‘yan kasa) suna son a magance matsalolin da ke shafar rayuwarsu ko a rage su. Suna son ingantacciyar rayuwa, ingantaccen kiwon lafiya, ilimi da tsaro.

Uba sani
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.