• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruɗani A Kan Shari’ar Abba Da Gawuna: Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar NNPP A Rubuce

bySulaiman
2 years ago
Nnpp

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan jihar Kano, Haruna Isah Dederi ya bayyana kurakuran da ke kunshe cikin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na tsige gwamna Abba Kabir Yusuf inda yace, hukuncin da kotun ta ayyana da baki ya sha bamban da tabbataccen Kwafin hukuncin da kotun ta mikawa gwamnatin Kano.

Ya bayyana haka ne da yammacin ranar Talata yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai kan hukuncin.

  • Za Mu Kwato Wa Abba Hakkinsa A Kotun Koli – NNPP
  • NNPP Ta Yi Maraba Da Kiran Atiku Na Dunkulewar Jam’iyyun Adawa Don Kauda APC

“An yanke hukunci game da dukkan kararraki hudu da muka daukaka, wanda mai girma Gwamna ya shigar, da karar da jam’iyyarmu ta NNPP ta shigar da karar da INEC ta shigar. Duk wadannan ukun an daukakasu ne saboda rashin amincewarsu da sakamakon hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta yanke a ranar 20 ga watan Satumba.

“karar ta hudu, itace wacce jam’iyyar APC ta yi. Duk waɗannan kararraki an sauraresu kuma an an yanke hukuncin kowacce.

“A ranar 17 ga watan Nuwamba, ranar Juma’a ne kotun daukaka kara ta karanta hukuncin. Wanda Yanzu haka kuma, aka bamu kwafin hukuncin daga kotun.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

“Abin takaici dangane da karar da gwamna ya shigar, mun gano cewa, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe.

“Ina ganin akwai tarko a nan. A yayin da muke zaman kotun an shaida mana cewa, an tabbatar da hukuncin da kotun farko ta yanke, amma a tabbataccen Kwafin takardun hukuncin game da daukaka karar da mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigar kan jam’iyyar APC da wasu mutane biyu, ya nuna cewa, kotun ta jingine hukuncin kotun farko a gefe, hakan na kunshe ne a shafi na 67 na kwafin hukuncin.

“Har yanzu ba mu san hukuncin da aka yanke ba kenan dangane da korafe-korafenmu. Tuni dai lauyoyinmu suka fara daukar mataki dangane da hakan na shigar da kara a gaban kotun koli dangane da hukuncin kotun daukaka kara,” inji shi.

Ya bayyana cewa, da abin da ke kunshe a cikin Tabbataccen hukuncin da kotun daukaka kara ta ba su, Abba Kabir Yusuf shine halastaccen gwamnan jihar Kano kamar yadda kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe yanke a farkon watan Satumba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Adamawa

Yadda Aka Farmaki Hedikwatar 'Yansanda A Adamawa  -Kwamishinan 'Yansanda Ya Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version