ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruɗani A Kan Shari’ar Abba Da Gawuna: Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar NNPP A Rubuce

by Sulaiman
3 years ago
Nnpp

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan jihar Kano, Haruna Isah Dederi ya bayyana kurakuran da ke kunshe cikin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke na tsige gwamna Abba Kabir Yusuf inda yace, hukuncin da kotun ta ayyana da baki ya sha bamban da tabbataccen Kwafin hukuncin da kotun ta mikawa gwamnatin Kano.

Ya bayyana haka ne da yammacin ranar Talata yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai kan hukuncin.

  • Za Mu Kwato Wa Abba Hakkinsa A Kotun Koli – NNPP
  • NNPP Ta Yi Maraba Da Kiran Atiku Na Dunkulewar Jam’iyyun Adawa Don Kauda APC

“An yanke hukunci game da dukkan kararraki hudu da muka daukaka, wanda mai girma Gwamna ya shigar, da karar da jam’iyyarmu ta NNPP ta shigar da karar da INEC ta shigar. Duk wadannan ukun an daukakasu ne saboda rashin amincewarsu da sakamakon hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta yanke a ranar 20 ga watan Satumba.

ADVERTISEMENT

“karar ta hudu, itace wacce jam’iyyar APC ta yi. Duk waɗannan kararraki an sauraresu kuma an an yanke hukuncin kowacce.

“A ranar 17 ga watan Nuwamba, ranar Juma’a ne kotun daukaka kara ta karanta hukuncin. Wanda Yanzu haka kuma, aka bamu kwafin hukuncin daga kotun.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Abin takaici dangane da karar da gwamna ya shigar, mun gano cewa, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe.

“Ina ganin akwai tarko a nan. A yayin da muke zaman kotun an shaida mana cewa, an tabbatar da hukuncin da kotun farko ta yanke, amma a tabbataccen Kwafin takardun hukuncin game da daukaka karar da mai girma gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigar kan jam’iyyar APC da wasu mutane biyu, ya nuna cewa, kotun ta jingine hukuncin kotun farko a gefe, hakan na kunshe ne a shafi na 67 na kwafin hukuncin.

“Har yanzu ba mu san hukuncin da aka yanke ba kenan dangane da korafe-korafenmu. Tuni dai lauyoyinmu suka fara daukar mataki dangane da hakan na shigar da kara a gaban kotun koli dangane da hukuncin kotun daukaka kara,” inji shi.

Ya bayyana cewa, da abin da ke kunshe a cikin Tabbataccen hukuncin da kotun daukaka kara ta ba su, Abba Kabir Yusuf shine halastaccen gwamnan jihar Kano kamar yadda kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe yanke a farkon watan Satumba.

NNPP
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Adamawa

Yadda Aka Farmaki Hedikwatar 'Yansanda A Adamawa  -Kwamishinan 'Yansanda Ya Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.