• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Babin Diflomasiyyar: Kira Ga Hadin Kai Da Zaman Lafiya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabon Babin Diflomasiyyar: Kira Ga Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin shekaru 60 da suka gabata, kasashen Sin da Faransa sun raya ingataccen hadin gwiwa a fannoni da dama, da suka shafi makamashin nukiliya, da jirgin kasa mai saurin tafiya, da sararin samaniya, da aikin gona, da kiwon lafiya da dai sauransu, wadanda suka samar da fa’ida ta zahiri ga jama’ar kasashen biyu.

A halin yanzu, Sin da Faransa dukkansu suna kan kololuwar matsayi a tarihin ci gaban kasa. Kasar Sin ta hanzarta samar da sabon tsarin ci gaba, da neman bunkasuwa mai inganci yayin da ta mai da hankali matuka kan muhimman batutuwa da suka hada da bunkasa sabon tsarin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da sabunta tsarin masana’antu, da farfado da yankunan karkararta, da samar da ci gaban hadin gwiwa a shiyya. yayin da ita kuma kasar Faransa take fama da batutuwa masu mahimmanci, gami da sauyin makamashi, da sauyi zuwa hada-hadar dijital da karuwan tsofaffi.

  • Manzon Musaman Na Shugaba Xi Jinping Ya Halarci Taron Koli Na Kungiyar Hadin Kan Kasashen Musulmi Karo Na 15
  • An Gabatar Da Shirin Bidiyo Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Wasu Muhimman Kafafen Yada Labaran Faransa

A wannan halin sauye-sauye da duniya ke fuskanta kamata ya yi bangarorin biyu su hanzarta yin hadin gwiwa a fannonin bunkasa fasahar kere-kere, da tattalin arzikin dijital, da masana’antun masu kiyaye muhalli, da ci gaba mai dorewa, da kara inganta hadin gwiwar aikin gona. Wannan yunkurin zai karfafa hadin kai tsakanin tsarin gudanar da masana’antu, saukake samar da jari da habaka mu’amalar ma’aikata, da zaman lafiya.

Bisa gayyatar da shugaba Emmanuel Macron na Jamhuriyar Faransa, da shugaban kasar Serbia Aleksandar Vucic, da takwaransa Tamas Sulyok da firaministan kasar Hungary Viktor Orban suka yi masa, shugaba Xi Jinping zai kai ziyarar aiki a kasashen Faransa, Serbia da Hungary daga ranar 5 ga watan Mayu zuwa 10. Ana sa ran ziyarar ta shugaba Xi a Faransa za ta haifar da wani sabon kuzari ga hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Faransa a fannonin da na ambato, tare da ba da jagoranci ga kasashen biyu wajen gano sabbin fannoni da hanyoyin hadin gwiwa cikin kankanin lokaci.

Shekaru 60 da suka gabata, janar de Gaulle ya bijirewa matsin lamba na kasashen yammacin Turai, ta hanyar kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Faransa. Inda daga bisani ya yi hasashen cewa “Hakika a bayyane yake cewa, dole ne Faransa ta yi mu’amala ta fahimtar juna da Sin kai tsaye, kuma ta tabbata kasar Sin ta yi mu’amala da ita”, wanda hakan ya jadadda jaruntaka, jajircewa, da hikimar da ke da ma’ana a duniyarmu ta yau. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CGTNCMGCRI Hausa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Ƙaryata Batun Kafa Sansanin Sojin Amurka Da Faransa A Ƙasarta

Next Post

Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi – Minista

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

17 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

17 hours ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

18 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

19 hours ago
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

21 hours ago
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

23 hours ago
Next Post
Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi – Minista

Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi - Minista

LABARAI MASU NASABA

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.