ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi – Minista

by Sulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kafafen yaɗa labarai wani babban ginshiƙi ne na haɓaka muhalli tare da kare martabar mulkin dimokiraɗiyya.

Ministan ya faɗi haka ne a lokacin bikin ba shi lambar yabo a wani ɓangare na Ranar ‘Yancin Aikin Jarida wanda aka yi a Abuja.

  • Gwamnatin Katsina Ta Ɗauki Ma’aikata 304 Don Kula Da Zirga-zirgar Ababen Hawa A Jihar
  • An Bukaci Manoma Su Kara Yawan Kwakwar Manjan Da Suke Nomawa

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) ita ce ta karrama shi da lambar.

ADVERTISEMENT

A jawabin sa jim kaɗan bayan ya karɓi lambar, Idris ya bayyana farin ciki da karramawar, musamman ganin ayyukan da ya yi da muƙaman da ya riƙe a fagen aikin jarida kafin a naɗa shi minista.

Ya ce: “Wannan karramawa ta yi min sosai, wanda ke da muhimmanci a kai na da kuma gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

“Wannan kyakkyawan karimcin zai zaburar da ni na sake sadaukar da kai ga hidimar al’ummar mu mai girma da kuma bil’adama baki ɗaya.”

Da yake magana kan taken bana na Ranar ‘Yancin Aikin Jarida, wato “Jarida ta Duniya: Aikin Jarida a Yayin da ake Fuskantar Matsalar Muhalli,” sai ministan ya ce, “A yayin da ake fuskantar matsalar muhalli, ’yan jarida sun kasance masu kula da gaskiya da kuma masu fafutikar tabbatar da gaskiya. Suna ƙarin haske kan rashin adalci na muhalli, suna fallasa ayyukan da ba daidai ba, da kuma ɗaga muryar waɗanda lalacewar muhalli ta fi shafa. Ta hanyar rahoton binciken su, suna ɗaukar gwamnatoci da ƙungiyoyin kamfanoni alhakin ayyukan su da bayar da shawarar manufofin da ke haɓaka ɗorewa da kiyaye duniyar mu.

“Taken taron na bana ya yi tasiri sosai kan manufofin ma’aikatar mu da kuma batutuwan da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sa a gaba, waɗanda suka haɗa da maido da amana, sake daidaita ƙimar ƙasa, da samar da yanayi mai kyau ga kafafen yaɗa labarai. Ya jaddada muhimmancin aikin jarida wajen magance matsalar muhalli.”

Ya ƙara da cewa, “A cikin tarihi, kafofin watsa labarai, a matsayin masu kula da gaskiya kuma masu samar da sauyi na zamantakewa, sun yi tsayin daka don yin la’akari, suna shawagi a kan ayyukan mutane, gwamnatoci, da kamfanoni.

“A wannan lokaci na rikicin muhalli, aikin watsa labarai ya wuce bayar da rahoto kawai; ya na ƙunshe ne da sadaukar da kai don shirya ayyukan gama-gari don amfanin jama’a. Tare da ikon faɗakarwa, ilmantarwa, da zaburarwa, kafofin watsa labarai su na da ikon da ba zai misaltu ba don kunna motsi, ɗaukaka muryoyi, da haifar da canjin ɗabi’a ga muhalli.”

Bugu da ƙari, Idris ya ce, “Yayin da mu ke bikin Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya, dole ne mu yi tunani a kan muhimmancin kafafen watsa labarai masu ‘yanci don bunƙasa mulkin dimokiraɗiyya, inganta gaskiya, da kuma kare haƙƙin bil’adama.

“Aikin jarida ya zama ginshiƙin tsarin dimokiraɗiyya ta hanyar samar da muhimmin dandali na yaɗa labarai, musayar ra’ayi, da kuma ɗora wa masu riƙe da madafun iko alhakin su.

“Kafafen yaɗa labarai na Nijeriya sun kasance masu fafutikar tabbatar da ɗorewar mulkin dimokiraɗiyya a ƙasar nan, kuma a irin wannan lokaci, mu na jinjina wa jajircewa da sadaukarwar ku kan aikin jarida.

“Duk da haka, yayin da mu ke murnar gudunmawar da ‘yan jarida ke bayarwa ga al’umma, mun kuma yarda da ƙalubalen da ‘yan jarida ke fuskanta wajen gudanar da muhimman ayyukan su. A matsayin su na masu kare muhalli, ‘yan jarida su kan fuskanci barazana, tsangwama, da tashin hankali saboda jajircewar su wajen fallasa laifukan muhalli da kare duniyar mu.”

Dangane da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya, ministan ya ce dole ne mu sake jaddada aniyar mu ta kare haƙƙin ‘yan jarida da tabbatar da tsaron su.

“A matsayi na na Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, ina so in ƙara jaddada aniyar mu ta kare ‘yancin aikin jarida, inganta ra’ayoyi mabambanta, da kare haƙƙin ‘yan jarida.

“Mu ƙara zage damtse wajen gina makoma inda aikin jarida zai bunƙasa, a tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida, da kuma kare duniyar mu har zuwa al’ummomi masu zuwa.

“Yayin da mu ke gudanar da ayyukan mu, dole ne mu kuma tuna cewa Nijeriya, muhallin mu, ita ce abin da ya kamata mu fara karewa daga labaran ƙarya.”

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya
Labarai

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Tattaunawa Da Macron

Xi Ya Yi Tattaunawa Da Macron

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.