• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Kwanturolan NIS A Ribas Ya Gargadi Jami’ansa Kan Bin Dokokin Aiki A Zaben 2023

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sabon Kwanturolan NIS A Ribas Ya Gargadi Jami’ansa Kan Bin Dokokin Aiki A Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon Kwanturolan hukumar kula da shige da fice (NIS) da aka tura jihar Ribas, CIS Sunday James, ya kama aiki gadan-gadan a shalkwatar hukumar da ke jihar tare da shan alwaashin inganta nagartar aiki a kowani lokaci.

Da ya ke ganawa da manyan jami’an hukumar a jihar ta Ribas, ya ja hankalinsu a kan bin matakan aiki tare da ka’idoji, kana ya bukaci kowani jami’in hukumar da ya gudanar da aikinsa yadda ya kamata yayin zaben 2023 da ke tafe ta hanyar gudanar da aiki bisa kwarewa da bin ka’idoji da dokokin aiki.

Sunday James ya gargadin dakarun nasa su nesanci shiga harkokin siyasa, yana mai cewa aikin da ke gabansu shi ne sanya ido da tabbatar da an gudanar da zaben nan cikin kwanciyar hankali kuma sahihi, amma kada wani a cikinsu ya nuna bangaranci ta siyasa a yayin da ke bakin aikinsa.

  • NIS Ta Sauyawa Wasu Manyan Jami’anta Jihohi Gabanin Zaben 2023

 

James ya tabbatar da cewa, NIS reshen jihar Ribas a shirye take wajen gudanar da aikin zaben 2023 kuma za ta tabbatar dukkanin wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, ba su samu shiga cikin harkokin zaben Nijeriya na 2023 ba, “Aikinmu shi ne mu tabbatar ‘yan kasashen waje (Wadanda ba ‘yan Nijeriya ba) ba su yi mana kazalandan a zaben 2023 ta hanyar ganin ba su samu damar jefa kuri’a ba.”

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

A wata sanarwar da sashin yada labarai na hukumar a jihar Ribas ya fitar a ranar Talata, ya bayyana cewar, manyan jami’an hukumar da suke shiyya-shiyya na hukumar a kananan hukumomi 23 da ke jihar sun hallara a shalkwatar inda sabon kwanturolan ya musu cikakken bayanin yadda za su kauce wa nuna bangaranci a siyasa kuma ya umarni su je su fada wa sauran jami’an da ke karkashinsu a kowani mataki domin tafiyar da aiki bisa ka’ida.

“Kwanturolan ya kuma shaida wa jami’an da su kasance cikin shiri tare da daukan matakan da suka dace na tsaro hadi da gaggawar kai rahoton abubuwan da ka iya tasowa domin daukan matakan da suka dace a kan lokacin domin inganta aikin da aka tura su a yayin zaben.”

Sanarwar ta kara da cewa, “Mista James ya amshi ragamar hukumar ne a hannun tsohon kwanturola, AJ Kwassau wanda yanzu aka masa karin girma zuwa mataimakin kwanturola janar ACG kuma yanzu haka shi ne mai kula da sashin bai wa ‘yan kasashen waje izinin aiki a kamfanoni da zuba hannun jari a Nijeriya (CERPAC) a shalkwatar hukumar NIS da ke Abuja.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Kori Karar Da Aka Shigar Kan Tsige Shugaban ‘Yansanda Na Kasa

Next Post

Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

10 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

11 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

16 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

18 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

18 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

21 hours ago
Next Post
Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.