• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Kwanturolan NIS A Ribas Ya Gargadi Jami’ansa Kan Bin Dokokin Aiki A Zaben 2023

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Sabon Kwanturolan NIS A Ribas Ya Gargadi Jami’ansa Kan Bin Dokokin Aiki A Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon Kwanturolan hukumar kula da shige da fice (NIS) da aka tura jihar Ribas, CIS Sunday James, ya kama aiki gadan-gadan a shalkwatar hukumar da ke jihar tare da shan alwaashin inganta nagartar aiki a kowani lokaci.

Da ya ke ganawa da manyan jami’an hukumar a jihar ta Ribas, ya ja hankalinsu a kan bin matakan aiki tare da ka’idoji, kana ya bukaci kowani jami’in hukumar da ya gudanar da aikinsa yadda ya kamata yayin zaben 2023 da ke tafe ta hanyar gudanar da aiki bisa kwarewa da bin ka’idoji da dokokin aiki.

Sunday James ya gargadin dakarun nasa su nesanci shiga harkokin siyasa, yana mai cewa aikin da ke gabansu shi ne sanya ido da tabbatar da an gudanar da zaben nan cikin kwanciyar hankali kuma sahihi, amma kada wani a cikinsu ya nuna bangaranci ta siyasa a yayin da ke bakin aikinsa.

  • NIS Ta Sauyawa Wasu Manyan Jami’anta Jihohi Gabanin Zaben 2023

 

James ya tabbatar da cewa, NIS reshen jihar Ribas a shirye take wajen gudanar da aikin zaben 2023 kuma za ta tabbatar dukkanin wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, ba su samu shiga cikin harkokin zaben Nijeriya na 2023 ba, “Aikinmu shi ne mu tabbatar ‘yan kasashen waje (Wadanda ba ‘yan Nijeriya ba) ba su yi mana kazalandan a zaben 2023 ta hanyar ganin ba su samu damar jefa kuri’a ba.”

Labarai Masu Nasaba

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

A wata sanarwar da sashin yada labarai na hukumar a jihar Ribas ya fitar a ranar Talata, ya bayyana cewar, manyan jami’an hukumar da suke shiyya-shiyya na hukumar a kananan hukumomi 23 da ke jihar sun hallara a shalkwatar inda sabon kwanturolan ya musu cikakken bayanin yadda za su kauce wa nuna bangaranci a siyasa kuma ya umarni su je su fada wa sauran jami’an da ke karkashinsu a kowani mataki domin tafiyar da aiki bisa ka’ida.

“Kwanturolan ya kuma shaida wa jami’an da su kasance cikin shiri tare da daukan matakan da suka dace na tsaro hadi da gaggawar kai rahoton abubuwan da ka iya tasowa domin daukan matakan da suka dace a kan lokacin domin inganta aikin da aka tura su a yayin zaben.”

Sanarwar ta kara da cewa, “Mista James ya amshi ragamar hukumar ne a hannun tsohon kwanturola, AJ Kwassau wanda yanzu aka masa karin girma zuwa mataimakin kwanturola janar ACG kuma yanzu haka shi ne mai kula da sashin bai wa ‘yan kasashen waje izinin aiki a kamfanoni da zuba hannun jari a Nijeriya (CERPAC) a shalkwatar hukumar NIS da ke Abuja.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Kori Karar Da Aka Shigar Kan Tsige Shugaban ‘Yansanda Na Kasa

Next Post

Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

1 hour ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

9 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

11 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

12 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

14 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

16 hours ago
Next Post
Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.