• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Kwanturolan NIS A Ribas Ya Gargadi Jami’ansa Kan Bin Dokokin Aiki A Zaben 2023

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sabon Kwanturolan NIS A Ribas Ya Gargadi Jami’ansa Kan Bin Dokokin Aiki A Zaben 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon Kwanturolan hukumar kula da shige da fice (NIS) da aka tura jihar Ribas, CIS Sunday James, ya kama aiki gadan-gadan a shalkwatar hukumar da ke jihar tare da shan alwaashin inganta nagartar aiki a kowani lokaci.

Da ya ke ganawa da manyan jami’an hukumar a jihar ta Ribas, ya ja hankalinsu a kan bin matakan aiki tare da ka’idoji, kana ya bukaci kowani jami’in hukumar da ya gudanar da aikinsa yadda ya kamata yayin zaben 2023 da ke tafe ta hanyar gudanar da aiki bisa kwarewa da bin ka’idoji da dokokin aiki.

Sunday James ya gargadin dakarun nasa su nesanci shiga harkokin siyasa, yana mai cewa aikin da ke gabansu shi ne sanya ido da tabbatar da an gudanar da zaben nan cikin kwanciyar hankali kuma sahihi, amma kada wani a cikinsu ya nuna bangaranci ta siyasa a yayin da ke bakin aikinsa.

  • NIS Ta Sauyawa Wasu Manyan Jami’anta Jihohi Gabanin Zaben 2023

 

James ya tabbatar da cewa, NIS reshen jihar Ribas a shirye take wajen gudanar da aikin zaben 2023 kuma za ta tabbatar dukkanin wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, ba su samu shiga cikin harkokin zaben Nijeriya na 2023 ba, “Aikinmu shi ne mu tabbatar ‘yan kasashen waje (Wadanda ba ‘yan Nijeriya ba) ba su yi mana kazalandan a zaben 2023 ta hanyar ganin ba su samu damar jefa kuri’a ba.”

Labarai Masu Nasaba

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

A wata sanarwar da sashin yada labarai na hukumar a jihar Ribas ya fitar a ranar Talata, ya bayyana cewar, manyan jami’an hukumar da suke shiyya-shiyya na hukumar a kananan hukumomi 23 da ke jihar sun hallara a shalkwatar inda sabon kwanturolan ya musu cikakken bayanin yadda za su kauce wa nuna bangaranci a siyasa kuma ya umarni su je su fada wa sauran jami’an da ke karkashinsu a kowani mataki domin tafiyar da aiki bisa ka’ida.

“Kwanturolan ya kuma shaida wa jami’an da su kasance cikin shiri tare da daukan matakan da suka dace na tsaro hadi da gaggawar kai rahoton abubuwan da ka iya tasowa domin daukan matakan da suka dace a kan lokacin domin inganta aikin da aka tura su a yayin zaben.”

Sanarwar ta kara da cewa, “Mista James ya amshi ragamar hukumar ne a hannun tsohon kwanturola, AJ Kwassau wanda yanzu aka masa karin girma zuwa mataimakin kwanturola janar ACG kuma yanzu haka shi ne mai kula da sashin bai wa ‘yan kasashen waje izinin aiki a kamfanoni da zuba hannun jari a Nijeriya (CERPAC) a shalkwatar hukumar NIS da ke Abuja.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Kori Karar Da Aka Shigar Kan Tsige Shugaban ‘Yansanda Na Kasa

Next Post

Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

Related

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

1 minute ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

31 minutes ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu
Labarai

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

2 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

11 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

13 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

16 hours ago
Next Post
Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.