ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Kwanturolan NIS A Ribas Ya Gargadi Jami’ansa Kan Bin Dokokin Aiki A Zaben 2023

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Ribas

Sabon Kwanturolan hukumar kula da shige da fice (NIS) da aka tura jihar Ribas, CIS Sunday James, ya kama aiki gadan-gadan a shalkwatar hukumar da ke jihar tare da shan alwaashin inganta nagartar aiki a kowani lokaci.

Da ya ke ganawa da manyan jami’an hukumar a jihar ta Ribas, ya ja hankalinsu a kan bin matakan aiki tare da ka’idoji, kana ya bukaci kowani jami’in hukumar da ya gudanar da aikinsa yadda ya kamata yayin zaben 2023 da ke tafe ta hanyar gudanar da aiki bisa kwarewa da bin ka’idoji da dokokin aiki.

Sunday James ya gargadin dakarun nasa su nesanci shiga harkokin siyasa, yana mai cewa aikin da ke gabansu shi ne sanya ido da tabbatar da an gudanar da zaben nan cikin kwanciyar hankali kuma sahihi, amma kada wani a cikinsu ya nuna bangaranci ta siyasa a yayin da ke bakin aikinsa.

ADVERTISEMENT
  • NIS Ta Sauyawa Wasu Manyan Jami’anta Jihohi Gabanin Zaben 2023

 

James ya tabbatar da cewa, NIS reshen jihar Ribas a shirye take wajen gudanar da aikin zaben 2023 kuma za ta tabbatar dukkanin wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, ba su samu shiga cikin harkokin zaben Nijeriya na 2023 ba, “Aikinmu shi ne mu tabbatar ‘yan kasashen waje (Wadanda ba ‘yan Nijeriya ba) ba su yi mana kazalandan a zaben 2023 ta hanyar ganin ba su samu damar jefa kuri’a ba.”

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A wata sanarwar da sashin yada labarai na hukumar a jihar Ribas ya fitar a ranar Talata, ya bayyana cewar, manyan jami’an hukumar da suke shiyya-shiyya na hukumar a kananan hukumomi 23 da ke jihar sun hallara a shalkwatar inda sabon kwanturolan ya musu cikakken bayanin yadda za su kauce wa nuna bangaranci a siyasa kuma ya umarni su je su fada wa sauran jami’an da ke karkashinsu a kowani mataki domin tafiyar da aiki bisa ka’ida.

“Kwanturolan ya kuma shaida wa jami’an da su kasance cikin shiri tare da daukan matakan da suka dace na tsaro hadi da gaggawar kai rahoton abubuwan da ka iya tasowa domin daukan matakan da suka dace a kan lokacin domin inganta aikin da aka tura su a yayin zaben.”

Sanarwar ta kara da cewa, “Mista James ya amshi ragamar hukumar ne a hannun tsohon kwanturola, AJ Kwassau wanda yanzu aka masa karin girma zuwa mataimakin kwanturola janar ACG kuma yanzu haka shi ne mai kula da sashin bai wa ‘yan kasashen waje izinin aiki a kamfanoni da zuba hannun jari a Nijeriya (CERPAC) a shalkwatar hukumar NIS da ke Abuja.”

Ribas
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

Bayanai Sun Fallasa Ikirarin Amurka Na Kare Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.