• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Layin Dogo Da Ya Zagaye Hamada Mafi Girma A Kasar Sin Ya Fara Aiki

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabon Layin Dogo Da Ya Zagaye Hamada Mafi Girma A Kasar Sin Ya Fara Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alhamis din nan ne, aka fara aiki da sashin karshe na layin dogo mai tsawon kilomita 2,712, wanda ya zagaye hamada mafi girma a kasar Sin, wato Taklamakan, dake yankin arewa maso yammacin jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta, bayan da aka shafe shekaru 3 da rabi ana kokarin ginawa.

Sabon sashin layin dogon mai nisan kilomita 825, ya tashi ne daga gabas da birnin Hotan zuwa gundumar Ruoqiang, kusa da gefen kudu da Taklamakan, hamada ta biyu mafi girma a duniya mai cike da yashi, inda kusan kashi 65 na layin dogo yake gudana cikin hamadar.
Bude layin dogo zai baiwa jiragen kasa damar zagaya da’irar hamadar dake zama karo na farko a duniya.

Haka kuma, layin dogon zai saukaka jigilar kayayyaki da tsare-tsaren wasu sana’o’i dake yankin Xinjiang da suka hada da auduga, da dangin gyada, da dabino, da ma’adinai.

A yau, fasinjoji sun yi tattaki zuwa tashar layin dogo da ke birnin Hotan, domin yin balaguro a karon farko a cikin wani jirgin kasa da ke gudun kilomita 120 a cikin sa’a guda, wanda kuma zai taimaka wajen saukaka tafiye-tafiye da inganta rayuwarsu.

Don taimakawa wajen kare hanyar dogon, an gina gadoji guda biyar, inda mafi tsayi daga cikinsu, ya kai fiye da kilomita 18, don daga layin dogon zuwa wani tsayin shinge wanda zai kare shi daga illar guguwar yashi.

Labarai Masu Nasaba

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Bugu da kari, an samar da wani ziri maras gurbata muhalli, mai kusan murabba’in mita miliyan 50 na ciyayi, inda aka shuka bishiyoyi miliyan 13, wadanda ake fatan za su ba da kariya ga sassan da ake ganin yashin zai iya yi musu illa.(Ibrahim)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kudirin Ba Dalibai Rancen Kudi Mara Ruwa Ya Tsallake Karatu Na 2 A Zauren Majalisar Dattijai

Next Post

Ya Kamata ‘Yan Siyasan Birtaniya Su Rika Yin Abu Gwargwadon Karfinsu

Related

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka
Daga Birnin Sin

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

7 hours ago
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

8 hours ago
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

8 hours ago
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe
Daga Birnin Sin

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

9 hours ago
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

10 hours ago
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya
Daga Birnin Sin

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

10 hours ago
Next Post
Ya Kamata ‘Yan Siyasan Birtaniya Su Rika Yin Abu Gwargwadon Karfinsu

Ya Kamata ‘Yan Siyasan Birtaniya Su Rika Yin Abu Gwargwadon Karfinsu

LABARAI MASU NASABA

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

September 2, 2025
Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

Gwamna Dauda Lawal A Shekara 60: Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

September 2, 2025
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

September 2, 2025
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

September 2, 2025
Gwamna Yusuf

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

September 2, 2025
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

September 2, 2025
Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

September 2, 2025
Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

Da Ɗum-ɗumi: Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

September 2, 2025
Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.