• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shugaban PDP Na Katsina Ya Nemi Haɗin Kai A Tsakanin ‘Ya’yan Jam’iyyar

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Siyasa
0
PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon shugaban jam’iyyar PDP mai adawa a jihar Katsina Alhaji Lawal Ɗanɓaci ya yi kira ga sauran ‘ya ‘yan jam’iyyar da su zo a yi aiki tare domin samun nasarar zaɓe a shekarar 2023.

  • Hedikwatar Tsaro Ta Ayyana Neman ‘Yan Ta’adda 19 Ruwa A Jallo, Ta Sa Ladar Miliyan 5 Kan Kowanne

Alhaji Lawal Ɗanɓaci ya yi wannan kira ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai jim kaɗan da shigarsa ofis a matsayin sabon shugaban jam’iyyar PDP na jihar Katsina wanda uwar jami’yya ta ƙasa ta naɗa

A cewar sa, ya hango nasara da duk wasu sharuɗa na cin zaɓe a shekarar 2023 shi yasa yake neman hadin kan ya yan jam’iyyar ta PDP domin yin aiki tare.

A cewar Alhaji Lawal Ɗanɓaci ya zo wannan shugabanci ne da kyakkyawan niya shi yasa ya ce duk inda ɗan PDP yake ya zo a dunkule waje guda.

Ya kara da cewa alamun nasarar da ya hango sun haɗa da yadda jami’yyar APC mai mulki ta jefa jama’a na yunwa da rashin tsaro da bala’o’i iri daban daban ya isa misalin abinda zai faru idan an zaɓe.

Labarai Masu Nasaba

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Alhaji Lawal Ɗanɓaci ya kafe akan cewa kowa yasan jami’yyar PDP jam’iyya ce ta adalci da girmamawa tare da ba kowa hakkin sa.

Sai dai ya cigaba da cewa zamba cikin aminci da yaudarar da jami’yyar APC ta yi al’umma a ƙasa da kuma jihar Katsina, jama’a na jiran ranar zaɓe domin zartar da hukunci daidai da laifi.

“insha’Allahu a shugabancina babu wani ɗan mowa ko ɗan bora zan kwatanta adalci wanda shi ne ginshikin cigaban kowace irin jami’yya ce kuma da shi ne ake samun nasara” inji shi.

Sabon shugaban jam’iyyar PDP ya ce don Allah a manta da duk wani rashin fahimta da ya faru ko yake faruwa a cikin jam’iyyar a matakin jihar Katsina, abinda kawai ya rage masu shine su tunkari yakin neman zaɓe.

Kazalika ya bayyana cewa kofa a buɗe take ga duk wani ɗan jami’yya da ke son bada shawara a kowane mataki, sannan ya yi kira ga ‘ya’yan jami’yyar da su san ya kishin jami’yyar PDP domin a cewar sa ita ke da nasara.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gabatar Da Bidiyon Musamman Na Bayanin Magabata Da Shugaba Xi Jinping Yake So Game Da Yadda Sin Ta Kama Sabuwar Hanyar Neman Samun Ci Gaba

Next Post

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Noma A Matsayin Dan Takarar PDP A Kebbi

Related

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

8 hours ago
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

2 days ago
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Siyasa

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2 days ago
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Siyasa

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

2 days ago
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

4 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

4 days ago
Next Post
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Noma A Matsayin Dan Takarar PDP A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.