• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabuwar Kasar Sin Ta Ba ‘Yan Uwanta Na Nahiyar Afirka Alfahari

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabuwar Kasar Sin Ta Ba ‘Yan Uwanta Na Nahiyar Afirka Alfahari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu shekaru 51 da suka wuce, wato a ranar 25 ga watan Oktoban shekarar 1971, aka zartas da wani kuduri a babban taron Majalisar Dinkin Duniya (MDD), inda aka maido da kujerar jamhuriyar jama’ar kasar Sin (sabuwar kasar Sin) a majalisar.

Wani bidiyon da aka dauka a lokacin ya nuna yadda wasu jami’an kasashen Afirka da suka halarci taron MDD suka yi matukar murnar ganin yadda sabuwar kasar Sin ta samu wannan nasara.

  • Masanan Afirka Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Tasirin Da Taron Wakilan JKS Karo Na 20 Zai Haifarwa Sin Da Duniya

Tsohon shugaban kasar Sin Mao Zedong ya taba bayyana cewa, ‘yan uwa na nahiyar Afirka sun dauki sabuwar kasar Sin, sun kai ta cikin MDD.

Hakika cikin kasashe 23 da suka gabatar da bukatar shigar da sabuwar kasar Sin cikin MDD, fiye da rabinsu kasashe ne daga nahiyar Afirka.

Sa’an nan, a lokacin da aka jefa kuri’a kan batun a majalisar, an jefa kuri’un amincewa 76, inda kuri’u 26, ko kuma mu ce kashi 1 bisa kashi 3 daga cikinsu, kuri’u ne da kasashen Afirka suka jefa.

Labarai Masu Nasaba

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Amma mene ne dalilin da ya sa kasashen Afirka suka nuna goyon baya ga sabuwar kasar Sin don ganin komawarta cikin MDD?

Shi ne domin a lokacin, ko da yake sabuwar ba a maido da kujerar kasar Sin cikin MDD ba tukuna, sakamakon yunkurin kasar Amurka na hana ruwa gudu game da batun, duk da haka, sabuwar kasar Sin ta yi kokarin kare adalci a duniya, inda kasar ta gabatar da ka’idoji biyar na zama tare cikin sulhu, da gina layin dogon da ya hada Tanzania da Zambia kyauta, da ba da taimako ga dimbin kasashen dake nahiyoyin Afirka, da Asia, da Latin Amurka, a fannin yakar ‘yan mulkin mallaka, da neman ‘yancin kansu.

Zuwa yanzu, wasu shekaru 51 sun shude. Idan aka waiwayi baya, ko zabin da kasashen Afirka suka yi ya yi daidai?

Za a tuna da cewa, cikin shekaru 51 da suka wuce, kasar Sin ta halarci kusan dukkan kungiyoyin kasa da kasa na tsakanin gwamnatoci, da sa hannu kan yarjeniyoyin kasa da kasa fiye da 600. Kana kasar ta zama ta biyu a fannin yawan samar da kudi ga MDD. Haka zalika, ta tura sojoji fiye da dubu 50, don gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a wurare daban daban na duniya.

Ba za a manta da yadda kasar Sin ta samar da gudunmowa ga aikin daidaita kundin tsarin MDD don tabbatar wa kasashe masu tasowa damar tura wakilansu don zama babban sakataren majalisar ba. Abin da ya daukaka matsayin kasashe masu tasowa, da ba su karin ikon fada a ji.

Sa’an nan a taron wakilan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin mai rike da ragamar mulki a kasar, Xi Jinping, babban magatakardan jam’iyyar, kana shugaban kasar Sin, ya nanata babbar manufar kasar Sin ta kare zaman lafiya a duniya, da baiwa kasashe daban daban damar samun ci gaba tare.

Hakan ma ya shaida muhimmiyar rawar da kasar Sin ke takawa a duniya, inda take kokarin neman ganin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya.

Vernon Mwanga, wani tsohon jami’in diplomasiya ne na kasar zambia, wanda ya taba jefa kuri’ar amincewa don taimakawa kasar Sin komawa cikin MDD. Yanzu, da ya waiwayi aikin da ya yi a lokacin, ya gaya ma ‘yan jaridu cewa, “wannan abun alfahari ne mafi muhimmanci da na taba yi a duk tsawon rayuwata”. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 5 Sun Mutu A Hartsarin Mota A Kaduna

Next Post

Mai Daki Shi Ya San Inda Yake Masa Yoyo

Related

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60
Daga Birnin Sin

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

51 minutes ago
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

21 hours ago
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

22 hours ago
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
Daga Birnin Sin

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

23 hours ago
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

1 day ago
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

2 days ago
Next Post
Mai Daki Shi Ya San Inda Yake Masa Yoyo

Mai Daki Shi Ya San Inda Yake Masa Yoyo

LABARAI MASU NASABA

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

August 5, 2025
Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60

August 5, 2025
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

August 5, 2025
Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

August 5, 2025
LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya

August 5, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

August 5, 2025
Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.