ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabuwar Kasar Sin Ta Ba ‘Yan Uwanta Na Nahiyar Afirka Alfahari

by CMG Hausa
4 years ago
Kasar Sin

Wasu shekaru 51 da suka wuce, wato a ranar 25 ga watan Oktoban shekarar 1971, aka zartas da wani kuduri a babban taron Majalisar Dinkin Duniya (MDD), inda aka maido da kujerar jamhuriyar jama’ar kasar Sin (sabuwar kasar Sin) a majalisar.

Wani bidiyon da aka dauka a lokacin ya nuna yadda wasu jami’an kasashen Afirka da suka halarci taron MDD suka yi matukar murnar ganin yadda sabuwar kasar Sin ta samu wannan nasara.

  • Masanan Afirka Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Tasirin Da Taron Wakilan JKS Karo Na 20 Zai Haifarwa Sin Da Duniya

Tsohon shugaban kasar Sin Mao Zedong ya taba bayyana cewa, ‘yan uwa na nahiyar Afirka sun dauki sabuwar kasar Sin, sun kai ta cikin MDD.

ADVERTISEMENT

Hakika cikin kasashe 23 da suka gabatar da bukatar shigar da sabuwar kasar Sin cikin MDD, fiye da rabinsu kasashe ne daga nahiyar Afirka.

Sa’an nan, a lokacin da aka jefa kuri’a kan batun a majalisar, an jefa kuri’un amincewa 76, inda kuri’u 26, ko kuma mu ce kashi 1 bisa kashi 3 daga cikinsu, kuri’u ne da kasashen Afirka suka jefa.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Amma mene ne dalilin da ya sa kasashen Afirka suka nuna goyon baya ga sabuwar kasar Sin don ganin komawarta cikin MDD?

Shi ne domin a lokacin, ko da yake sabuwar ba a maido da kujerar kasar Sin cikin MDD ba tukuna, sakamakon yunkurin kasar Amurka na hana ruwa gudu game da batun, duk da haka, sabuwar kasar Sin ta yi kokarin kare adalci a duniya, inda kasar ta gabatar da ka’idoji biyar na zama tare cikin sulhu, da gina layin dogon da ya hada Tanzania da Zambia kyauta, da ba da taimako ga dimbin kasashen dake nahiyoyin Afirka, da Asia, da Latin Amurka, a fannin yakar ‘yan mulkin mallaka, da neman ‘yancin kansu.

Zuwa yanzu, wasu shekaru 51 sun shude. Idan aka waiwayi baya, ko zabin da kasashen Afirka suka yi ya yi daidai?

Za a tuna da cewa, cikin shekaru 51 da suka wuce, kasar Sin ta halarci kusan dukkan kungiyoyin kasa da kasa na tsakanin gwamnatoci, da sa hannu kan yarjeniyoyin kasa da kasa fiye da 600. Kana kasar ta zama ta biyu a fannin yawan samar da kudi ga MDD. Haka zalika, ta tura sojoji fiye da dubu 50, don gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a wurare daban daban na duniya.

Ba za a manta da yadda kasar Sin ta samar da gudunmowa ga aikin daidaita kundin tsarin MDD don tabbatar wa kasashe masu tasowa damar tura wakilansu don zama babban sakataren majalisar ba. Abin da ya daukaka matsayin kasashe masu tasowa, da ba su karin ikon fada a ji.

Sa’an nan a taron wakilan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin mai rike da ragamar mulki a kasar, Xi Jinping, babban magatakardan jam’iyyar, kana shugaban kasar Sin, ya nanata babbar manufar kasar Sin ta kare zaman lafiya a duniya, da baiwa kasashe daban daban damar samun ci gaba tare.

Hakan ma ya shaida muhimmiyar rawar da kasar Sin ke takawa a duniya, inda take kokarin neman ganin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya.

Vernon Mwanga, wani tsohon jami’in diplomasiya ne na kasar zambia, wanda ya taba jefa kuri’ar amincewa don taimakawa kasar Sin komawa cikin MDD. Yanzu, da ya waiwayi aikin da ya yi a lokacin, ya gaya ma ‘yan jaridu cewa, “wannan abun alfahari ne mafi muhimmanci da na taba yi a duk tsawon rayuwata”. (Bello Wang)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
Daga Birnin Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
Daga Birnin Sin

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Next Post
Mai Daki Shi Ya San Inda Yake Masa Yoyo

Mai Daki Shi Ya San Inda Yake Masa Yoyo

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

June 21, 2026
Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna

June 21, 2026
Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi

June 21, 2026
FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa

June 21, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran

June 21, 2026
‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.