• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sake Gina Aminci Tsakanin Sin Da Amurka Zai Amfani Duniya Baki Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sake Gina Aminci Tsakanin Sin Da Amurka Zai Amfani Duniya Baki Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya bayan nan, ana ta ganin karuwar sabani, da rashin daidaito ta fuskar alakar Sin da Amurka, wanda hakan ke da matukar hadari ga dunkulewar duniya da cimma nasara tare.

 

A halin yanzu, yanayin alakar kasashen biyu na cike da kalubale, ya kuma gaza hawa turba mai inganci da za ta haifar da moriya ga sassa biyu da ma duniya baki daya. Hakan ya sa masharhanta ke ganin lokaci ya yi manyan kasashen biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, za su rungumi hanyoyin da ba na fito na fito ba, wajen shawo kan mummunar takara, su kuma amince da tafarki guda na cimma nasara wadda kowa zai ci gajiyarta.

  • Xi Ya Taya Trump Murnar Lashe Zaben Shugaban Amurka
  • Sin Ta Yi Alkawarin Fadada Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Kasa Da Kasa

A ganina, hanya daya tilo ta kaiwa ga cimma wannan nasara ita ce dukkanin sassan biyu su amine cewa za su iya bin hanyoyin cimma daidaito cikin lumana, da tattaunawa, wadanda za su dace da zaman jituwa da moriyarsu.

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yayin da Sin da Amurka ke kara fadada tasirinsu ta hanyar karfafa alaka da sauran sassan duniya, fifikon Amurka shi ne karfin ikon ayyukan soji, da samar da kariyar tsaro ga kawayenta da tasiri a siyasar duniya. A hannu guda kuwa, kasar Sin na mayar da hankali ne ga fadada zaman jituwa, da zuba jari, da ingiza cinikayya tsakaninta da sauran kasuwannin duniya.

 

Kafin shekarar 2001, wato shekarar da kasar Sin ta shiga kungiyar cinikayya ta duniya ko WTO, kaso 80 bisa dari na kasashen duniya suna gudanar da hada-hadar cinikayya ne da Amurka sama da yadda suke yi da kasar Sin. Amma a yau, manufofin kasar Sin irin su shawarar nan ta “Ziri daya da hanya daya, sun haifar da fadadar cinikayya tsakanin Sin da kasashen duniya 128 cikin 190 sama da yadda suke yi da Amurka.

 

Nan gaba kadan za a kafa sabuwar gwamnatin Amurka, kuma fatan al’ummun duniya shi ne wannan sabuwar gwamnati ta zo da tsarin sassanta alaka da Sin, ta yadda hadin gwiwarsu za ta ingiza daidaito, da ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya. Kana duniya ta ci gajiya daga nasarar da kyautatuwar alakar manyan kasashen biyu za ta haifar. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabuwar Ƙungiya Ƴan Ta’adda Ta Ɓulla A Sokoto – Shalƙwatar Tsaro 

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 481, Sun Kama Wasu 741, Sun Ceto Mutane 492 A Watan Oktoba

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

28 minutes ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

1 hour ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

3 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

4 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

12 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

13 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 481, Sun Kama Wasu 741, Sun Ceto Mutane 492 A Watan Oktoba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 481, Sun Kama Wasu 741, Sun Ceto Mutane 492 A Watan Oktoba

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.