• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sallama Da 2024: Yadda Sin Ta Gudanar Da Diflomasiyya Ta Zaman Lafiya Ba Tayar Da Husuma Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sallama Da 2024: Yadda Sin Ta Gudanar Da Diflomasiyya Ta Zaman Lafiya Ba Tayar Da Husuma Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An ce idan aski ya zo gaban goshi ya fi zafi, tun da shekarar 2024 ta fara yin adabo, kasashe na ta yi wa kansu hisabi a kan abubuwan da suka shuka a cikin shekarar. Na tabbatar da cewa, wadanda suka shuka alheri ko gizau, daidai da kwayar gashin girarsu daya ba ta karaya ba. Haka nan ’yan baya-ga-dangi masu tafka ta’asa su ma sun san kansu, domin kowa ya gyara ya sani, kazalika kowa ya bata ya sani.

A yayin da wasu kasashe musamman masu karfin fada-a-ji a duniya suke taimakawa da makamai wajen yi wa al’ummar da ba ta ji ba, ba ta gani ba kisan kiyashi, ita kuwa kasar Sin ta nuna himma wajen shimfida fukafukanta ga sassan duniya wajen samar da ci gaba da raya duniya da tsare-tsare mafiya dacewa da zamanin da muke ciki.

  • Wannan Jawabi Ya Karfafa Zuciyarmu a Fannoni Uku
  • Tashar Samar Da Wutar Lantarki Mai Amfani Da Karfin Ruwa Mafi Girma a Duniya Ta Fara Aiki

A shekarar 2024, kasar Sin ta karbi bakuncin manyan tarurruka na hadin gwiwa da shugabannin kasashen duniya kamar su taron dandalin hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa a watan Mayu, da babban taron cika shekaru 70 da kafa ka’idojin dorewar zaman lafiya a watan Yuni da kuma taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka a watan Satumba.

Kazalika, daga waje, Shugaba Xi Jinping na kasar ya kai ziyarce-ziyarce masu muhimmanci kasashen ketare da suka hada da yankin Turai a watan Mayu, yankin tsakiyar Asiya a watan Yuli da yankin Latin na Amurka a Nuwamba, baya ga taron kawancen kasashen BRICKS da ya halarta a watan Oktoba.

Duka a tarurrukan da kasar Sin ta karbi bakuncinsu a cikin gida ko shugabanninta suka halarta a ketare, an mayar da hankali a kan kyautata hulda da hadin gwiwar samar da ci gaba mai gamewa da kuma wanzuwar adalci a tsakanin kasashe da shugabancin duniya.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

A karon farko a yankin Turai, kasar Serbia ta amince da shiga kokarin gina al’umma mai makoma ta bai-daya a sabon zamani. Bugu da kari, Sin ta bude sabon babi na huldarta da Faransa yayin da Shugaba Xi ya ziyarci kasar a watan Mayu. Haka nan, ta daga darajar alakarta da Hungary, baya ga ci gaba da tuntubar juna da tattaunawa da sauran kasashen yankin kamar su Jamus, Birtaniya, Spain, Italiya da hatta Amurka ma Sin ta nemi kara kyautata huldodinsu cikin lumana yayin da Shugaba Xi da Shugaba Biden suka yi ganawar keke-da-keke a birnin Lima na Peru a watan Nuwamba, a gefen taron APEC.

Kazalika, Sin da Afirka sun dora tubali na gina al’umma mai makoma ta bai-daya a dukkan sassa da zai game mutanensu biliyan 2.8.

A yankin makwabta ma, alakar Sin da kasashe ta kara karfi inda aka fara wata sabuwar kyakkyawar hulda tsakanin Sin da Vietnam a shekarar ta 2024. Haka nan, fitar farko zuwa waje da zababben shugaban kasar Indonesia Prabowo Subianto ya yi, ita ce zuwa kasar Sin a watan Oktoba. Kana, Sin da Malaysia sun yi bikin cikar huldarsu ta diflomasiyya shekaru 50 da kafuwa, sannan alakar kasar da sauran kasashe irin su Singapore, Laos da Cambodia duka sun inganta cikin zurfafawa. Yayin da har ila yau, manyan kasashen yankin irin su Japan da Indiya duka suka amince su rika tuntubar juna da wanzar da zaman lafiya a kan iyakokinsu. Sakamakon haka ne Sin da Japan suka amince su gaggauta aiwatar da shawarar da aka cimma dangane da fitar da dagwalon masana’antu na Fukushima ba tare da bata lokaci ba, yayin da Shugaba Xi ya gana da firaministan Japan Shigeru Ishiba, a gefen taron shugabannin mambobin APEC karo na 31.

Kasar Sin ta kasance a gaba wajen yekuwar hawa teburin sulhu da tattaunawa maimakon fito-na-fito kan duk wata mas’ala da ta taso a duniya har ma ya kai ga babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 78 ya amince da kudurin da Sin ta gabatar na kebe ko wace ranar 10 ga Yuni ta zama ranar tattaunawa a tsakanin wayewar kai da al’adu na mabambantan kasashe.

Haka nan, ta rika kai goro-ta-kai-mari wajen tabbatar da amincewar kudurin tsagaita bude wuta a yankin Gaza na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, da sulhunta bangarorin Falasdinawa da kaddamar da kungiyar “abokan neman zaman lafiya” dangane da rikicin Ukraine.

Domin dorewar ci gaban duniya da kawo sauyi mai ma’ana, Shugaba Xi ya nanata matsayin Sin na bin turbar zaman lafiya a ko yaushe, yayin da yake maraba da jakadun kasashe 28 da suka fara aiki a kasar Sin a watan Disambar 2024. Inda hakan ya nuna bambanci a fili tsakanin Sin da manyan kasashe masu tayar da husuma a kan iyakokin teku, da bayar da makamai na kisan kare dangi a yankunan da ake rikici da zama kanwa-uwar-gamin galibin fitintinun da ake fama da su a duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Tsaro: Ribaɗu Ya Yaba Wa Sojoji, ‘Yansanda, DSS, Da Sauran Hukumomin Tsaro

Next Post

Sin Za Ta Yi Hadin Gwiwar Aiki Da Sauran Kasashe Masu Tasowa Domin Samar Da Ci Gaba

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

6 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

7 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

8 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

9 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

10 hours ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

13 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Yi Hadin Gwiwar Aiki Da Sauran Kasashe Masu Tasowa Domin Samar Da Ci Gaba

Sin Za Ta Yi Hadin Gwiwar Aiki Da Sauran Kasashe Masu Tasowa Domin Samar Da Ci Gaba

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.