ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Jawabi Ya Karfafa Zuciyarmu a Fannoni Uku

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Jawabi

Jiya Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabin taya murnar shiga sabuwar shekara ta 2025, inda ya takaita nasarorin da kasarsa ta cimma a shekarar 2024, gami da bayyana burinta a sabuwar shekara. A ganina, wannan jawabi ya karfafa zuciyar mutane daga wasu fannoni uku.

Na farko, yana karfafa zuciyarmu kan tattalin arzikin Sin.

  • Rahoto: Sana’ar Watsa Labarai Ta Kasar Sin Ta Shiga Zamanin Cudanyar Digital Da Basira
  • Takardun Kuɗi Sun Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 4.8 Duk Da Ƙarancin Kuɗi A Nijeriya

Ta la’akari da matsayin kasar Sin na babbar kawar kasashen Afirka a fannin hadin gwiwar tattalin arziki, babu shakka, yanayin ci gaban tattalin arzikin Sin yana haifar da babban tasiri kan nahiyar Afirka. To ko ta yaya tattalin arzikin kasar yake a shekarar 2024? Za a samu amsa cikin jawabin shugaba Xi, inda ya ce tattalin arzikin kasarsa ya samu farfadowa sosai: An yi hasashen cewa, GDPn kasar zai kai fiye da dalar Amurka tiriliyan 17.8, yayin da yawan hatsin da aka samar a kasar zai wuce ton miliyan 700, duk a shekarar ta 2024. Ban da haka, yunkurin wasu kasashen yamma na hana Sin samun ci gaba ta fuskar kimiyya da fasaha ya ci tura, ganin yadda kasar ta samu ci gaba sosai a fannin sabbin sana’o’i da masana’antu. A bara, yawan motoci masu amfani da wutar lantarki da aka samar a kasar Sin ya zarce miliyan 10 a karon farko, kana kasar ta samu dimbin sakamako a fannonin fasahohin kwaikwayon tunanin dan Adam na AI, da na zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya, da dai makamantansu.

ADVERTISEMENT

Na biyu, jawabin shugaba Xi ya sa mutane jin karfin zuci kan huldar dake tsakanin bangarorin Sin da Afirka.

Cikin jawabinsa, shugaban na kasar Sin ya ambaci yadda kasar ta karbi bakuncin taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka FOCAC, da kokarin aiwatar da shirin raya “Ziri Daya da Hanya Daya”, duk a shekarar ta bara.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Hakika taron koli na FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a wannan karo yana da ma’ana sosai. Saboda a wajen taron, an daga matsayin huldar dake tsakanin kasar Sin da dukkan kasashen Afirka da ta kulla huldar diplomasiyya da su, zuwa hulda mai muhimmanci da ta shafi manyan tsare-tsare, kana an sanar da dimbin shirye-shiryen ayyuka na zamanantar da Afirka, manya da kanana. A shekarar 2025 za a yi kokarin aiwatar da wadannan ayyukan da aka tsara.

Sa’an nan na uku shi ne, jawabin shugaba Xi ya ba mu kwarin gwiwa dangane da makomar kasashe masu tasowa, wato Global South.

Shugaba Xi ya ambata a cikin jawabinsa, kokarin da kasar Sin ta yi, wajen ingiza gyare-gyare a fannin gudanar da al’amuran duniya, da zurfafa hadin gwiwar kasashe masu tasowa, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. Kana ya gabatar da dabarar da za a iya bi, domin tinkarar kalubalolin da ake fuskantar a duniya, wato nuna hakuri da karamci don daidaita sabanin ra’ayi, da dora muhimmanci kan makomar dan Adam maimakon moriyar kai. Hakika, kasashe masu tasowa ne kadai ke iya daukar wannan dabara.

A shekarar 2024, yayin da wasu kasashen dake yammacin duniya ke neman katse huldar hadin kan kasa da kasa, da haifar da cikas ga tsarin dunkulewar kasuwannin duniya, mun shaida yadda aka habaka tsarin hadin gwiwa na BRICS, da yadda kungiyar kasashen Afirka ta AU ta halarci taron kolin G20 a matsayin mambar rukunin, da ma yadda aka shirya manyan tarukan kasa da kasa da dama a wasu kasashe masu tasowa, da suka hada da Peru da Brazil. Ban da haka, mun gane ma idanunmu yadda kasashen Afirka da kasar Sin suka zartas da ‘Sanarwar Beijing’, don bayyana kin yarda da ra’ayin nuna fin karfi, da yunkurin ta da rikici tsakanin rukunoni daban daban. Tabbas za mu ga yadda Sin da Afirka, tare da sauran kasashe masu tasowa, suka ci gaba da kokarin kare moriyar bai daya, da adalci, a shekarar 2025.

Kamar yadda shugaba Xi ya fada, ”Za a iya cimma duk wani buri, matukar ana kokarin nema.” Ina da imani kan cewar, hadin kan Sin da Afirka, da na dukkan kasashe masu tasowa baki daya, za su tabbatar da cikar burin kasar Sin da na kasashen Afirka, na samun zamanantarwa da ci gaban tattalin arziki. (Bello Wang)

Jawabi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Jawabi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Kano

Gwamnatin Kano Ta Yi Fatali Da Kudirin Sake Fasalin Dokar Haraji

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.