ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Jawabi Ya Karfafa Zuciyarmu a Fannoni Uku

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Jawabi

Jiya Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabin taya murnar shiga sabuwar shekara ta 2025, inda ya takaita nasarorin da kasarsa ta cimma a shekarar 2024, gami da bayyana burinta a sabuwar shekara. A ganina, wannan jawabi ya karfafa zuciyar mutane daga wasu fannoni uku.

Na farko, yana karfafa zuciyarmu kan tattalin arzikin Sin.

  • Rahoto: Sana’ar Watsa Labarai Ta Kasar Sin Ta Shiga Zamanin Cudanyar Digital Da Basira
  • Takardun Kuɗi Sun Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 4.8 Duk Da Ƙarancin Kuɗi A Nijeriya

Ta la’akari da matsayin kasar Sin na babbar kawar kasashen Afirka a fannin hadin gwiwar tattalin arziki, babu shakka, yanayin ci gaban tattalin arzikin Sin yana haifar da babban tasiri kan nahiyar Afirka. To ko ta yaya tattalin arzikin kasar yake a shekarar 2024? Za a samu amsa cikin jawabin shugaba Xi, inda ya ce tattalin arzikin kasarsa ya samu farfadowa sosai: An yi hasashen cewa, GDPn kasar zai kai fiye da dalar Amurka tiriliyan 17.8, yayin da yawan hatsin da aka samar a kasar zai wuce ton miliyan 700, duk a shekarar ta 2024. Ban da haka, yunkurin wasu kasashen yamma na hana Sin samun ci gaba ta fuskar kimiyya da fasaha ya ci tura, ganin yadda kasar ta samu ci gaba sosai a fannin sabbin sana’o’i da masana’antu. A bara, yawan motoci masu amfani da wutar lantarki da aka samar a kasar Sin ya zarce miliyan 10 a karon farko, kana kasar ta samu dimbin sakamako a fannonin fasahohin kwaikwayon tunanin dan Adam na AI, da na zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya, da dai makamantansu.

ADVERTISEMENT

Na biyu, jawabin shugaba Xi ya sa mutane jin karfin zuci kan huldar dake tsakanin bangarorin Sin da Afirka.

Cikin jawabinsa, shugaban na kasar Sin ya ambaci yadda kasar ta karbi bakuncin taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka FOCAC, da kokarin aiwatar da shirin raya “Ziri Daya da Hanya Daya”, duk a shekarar ta bara.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Hakika taron koli na FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a wannan karo yana da ma’ana sosai. Saboda a wajen taron, an daga matsayin huldar dake tsakanin kasar Sin da dukkan kasashen Afirka da ta kulla huldar diplomasiyya da su, zuwa hulda mai muhimmanci da ta shafi manyan tsare-tsare, kana an sanar da dimbin shirye-shiryen ayyuka na zamanantar da Afirka, manya da kanana. A shekarar 2025 za a yi kokarin aiwatar da wadannan ayyukan da aka tsara.

Sa’an nan na uku shi ne, jawabin shugaba Xi ya ba mu kwarin gwiwa dangane da makomar kasashe masu tasowa, wato Global South.

Shugaba Xi ya ambata a cikin jawabinsa, kokarin da kasar Sin ta yi, wajen ingiza gyare-gyare a fannin gudanar da al’amuran duniya, da zurfafa hadin gwiwar kasashe masu tasowa, da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. Kana ya gabatar da dabarar da za a iya bi, domin tinkarar kalubalolin da ake fuskantar a duniya, wato nuna hakuri da karamci don daidaita sabanin ra’ayi, da dora muhimmanci kan makomar dan Adam maimakon moriyar kai. Hakika, kasashe masu tasowa ne kadai ke iya daukar wannan dabara.

A shekarar 2024, yayin da wasu kasashen dake yammacin duniya ke neman katse huldar hadin kan kasa da kasa, da haifar da cikas ga tsarin dunkulewar kasuwannin duniya, mun shaida yadda aka habaka tsarin hadin gwiwa na BRICS, da yadda kungiyar kasashen Afirka ta AU ta halarci taron kolin G20 a matsayin mambar rukunin, da ma yadda aka shirya manyan tarukan kasa da kasa da dama a wasu kasashe masu tasowa, da suka hada da Peru da Brazil. Ban da haka, mun gane ma idanunmu yadda kasashen Afirka da kasar Sin suka zartas da ‘Sanarwar Beijing’, don bayyana kin yarda da ra’ayin nuna fin karfi, da yunkurin ta da rikici tsakanin rukunoni daban daban. Tabbas za mu ga yadda Sin da Afirka, tare da sauran kasashe masu tasowa, suka ci gaba da kokarin kare moriyar bai daya, da adalci, a shekarar 2025.

Kamar yadda shugaba Xi ya fada, ”Za a iya cimma duk wani buri, matukar ana kokarin nema.” Ina da imani kan cewar, hadin kan Sin da Afirka, da na dukkan kasashe masu tasowa baki daya, za su tabbatar da cikar burin kasar Sin da na kasashen Afirka, na samun zamanantarwa da ci gaban tattalin arziki. (Bello Wang)

Jawabi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Jawabi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Kano

Gwamnatin Kano Ta Yi Fatali Da Kudirin Sake Fasalin Dokar Haraji

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.