• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin zaman dandalin masana da kwararru na ’yan jaridu daga kasashe masu tasowa da masu saurin bunkasar tattalin arziki da ya gudana a birnin Sao Paulo na kasar Brazil a farkon makon nan, an fitar da rahoton hadin gwiwa mai taken “Sabon salon ci gaban bil Adama da muhimmancin hakan ga bunkasar duniya”. 

 

Rahoton wanda kwararru daga cibiyar nazarin tarihin JKS da binciken adabi, da hadin gwiwar kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua suka fitar, ya yi cikakken fashin baki game da ma’ana, da dabarun aiwatarwa, da muhimmancin dake kunshe cikin salon zamanantarwa irin na kasar Sin, tare da abun al’ajabi da kasar Sin ta cimma a fannin bunkasa rayuwar bil Adama.

  • EFCC Ta Kwace Fasfon Mataimakin Atiku A Zaɓen 2023
  • Nijeriya Na Buƙatar Maki 3 Yau Domin Samun Gurbi A Gasar Ƙasashen Afrika 

Idan mun yi nazari da kyau, za mu ga cewa wannan sabon salon samar da ci gaba dake kunshe cikin tsarin zamanantarwa irin na kasar Sin, ya yi daidai da burin kasar na ganin an shawo kan manyan kalubalolin dake addabar dan Adam a wannan karni na 21.

 

Labarai Masu Nasaba

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

A halin da duniya ke ci yanzu, sauye-sauye da suke faruwa sun tilasawa al’ummun duniya shiga wani yanayi mai sarkakiya, inda dukkanin sassa ke mayar da hankali ga tambaya kan abubuwan dake addabar duniya da abubuwan da ya dace a yi domin warware matsaloli, kasancewar hakan ne zai haifar da ci gaban da dan Adam ke fata, da kuma dorewar rayuwa mai inganci a yanzu da ma a nan gaba.

 

Bisa wannan buri, JKS ta jagoranci al’ummar Sinwa wajen samar da daidaiton ci gaba ta fuskar farfado da kai, da inganta tsarin siyasa, da raya al’adu, da zamantakewa, da kare muhalli da sauransu. Wannan sabuwar turba ta zamanantarwa irin ta Sin ta bayar da gudummawar kawar da gibin jagoranci, ta wanzar da aminci, da zaman lafiya da ci gaba, tare da samarwa duniya wata alkibla ta cimma zaman lafiya da makoma mai haske a fannin wayewar kan daukacin bil Adama.

 

A wannan gaba da kasar Sin mai al’ummun da yawansu ya haura biliyan 1.4 ke kan turbar zamanantar da kai, kasar na kan wata turba ta baiwa duniya kyakkyawan misalin zamanantarwa a sabon zamani.

 

Ko shakka babu cimma nasarar zamanantar da kai, buri ne na dukkanin kasashen duniya, kuma muddin duniya ta rungumi misalin irin nasarori da kasar Sin ta cimma a wannan fage hannu biyu, al’ummar duniya musamman kasashe masu tasowa, da su kai ga cimma burinsu na samun ci gaba yadda ya kamata.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Kwace Fasfon Mataimakin Atiku A Zaɓen 2023

Next Post

Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

Related

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

9 hours ago
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

10 hours ago
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

11 hours ago
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”
Daga Birnin Sin

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

12 hours ago
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

13 hours ago
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao
Daga Birnin Sin

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

13 hours ago
Next Post
Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.