• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin Riba Ce Ga Duniya Baki Daya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin zaman dandalin masana da kwararru na ’yan jaridu daga kasashe masu tasowa da masu saurin bunkasar tattalin arziki da ya gudana a birnin Sao Paulo na kasar Brazil a farkon makon nan, an fitar da rahoton hadin gwiwa mai taken “Sabon salon ci gaban bil Adama da muhimmancin hakan ga bunkasar duniya”. 

 

Rahoton wanda kwararru daga cibiyar nazarin tarihin JKS da binciken adabi, da hadin gwiwar kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua suka fitar, ya yi cikakken fashin baki game da ma’ana, da dabarun aiwatarwa, da muhimmancin dake kunshe cikin salon zamanantarwa irin na kasar Sin, tare da abun al’ajabi da kasar Sin ta cimma a fannin bunkasa rayuwar bil Adama.

  • EFCC Ta Kwace Fasfon Mataimakin Atiku A Zaɓen 2023
  • Nijeriya Na Buƙatar Maki 3 Yau Domin Samun Gurbi A Gasar Ƙasashen Afrika 

Idan mun yi nazari da kyau, za mu ga cewa wannan sabon salon samar da ci gaba dake kunshe cikin tsarin zamanantarwa irin na kasar Sin, ya yi daidai da burin kasar na ganin an shawo kan manyan kalubalolin dake addabar dan Adam a wannan karni na 21.

 

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

A halin da duniya ke ci yanzu, sauye-sauye da suke faruwa sun tilasawa al’ummun duniya shiga wani yanayi mai sarkakiya, inda dukkanin sassa ke mayar da hankali ga tambaya kan abubuwan dake addabar duniya da abubuwan da ya dace a yi domin warware matsaloli, kasancewar hakan ne zai haifar da ci gaban da dan Adam ke fata, da kuma dorewar rayuwa mai inganci a yanzu da ma a nan gaba.

 

Bisa wannan buri, JKS ta jagoranci al’ummar Sinwa wajen samar da daidaiton ci gaba ta fuskar farfado da kai, da inganta tsarin siyasa, da raya al’adu, da zamantakewa, da kare muhalli da sauransu. Wannan sabuwar turba ta zamanantarwa irin ta Sin ta bayar da gudummawar kawar da gibin jagoranci, ta wanzar da aminci, da zaman lafiya da ci gaba, tare da samarwa duniya wata alkibla ta cimma zaman lafiya da makoma mai haske a fannin wayewar kan daukacin bil Adama.

 

A wannan gaba da kasar Sin mai al’ummun da yawansu ya haura biliyan 1.4 ke kan turbar zamanantar da kai, kasar na kan wata turba ta baiwa duniya kyakkyawan misalin zamanantarwa a sabon zamani.

 

Ko shakka babu cimma nasarar zamanantar da kai, buri ne na dukkanin kasashen duniya, kuma muddin duniya ta rungumi misalin irin nasarori da kasar Sin ta cimma a wannan fage hannu biyu, al’ummar duniya musamman kasashe masu tasowa, da su kai ga cimma burinsu na samun ci gaba yadda ya kamata.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Kwace Fasfon Mataimakin Atiku A Zaɓen 2023

Next Post

Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

18 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

19 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

20 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

21 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

23 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

2 days ago
Next Post
Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

Binciken Ra’ayoyin Al’umma Ya Nuna Akwai Bukatar Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi Cikin Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.