• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar ci gaban da kasar Sin ta samu musamman a gwamman shekarun da suka gabata, tilas ya amince cewa salon da kasar ke bi wajen zamanantar da kai ya ciri tuta, duba da yadda ya haifarwa ’yan kasar da mai ido ta fuskar tsame alumma daga kangin talauci, da samarwa alummar Sinawa damar more ababen more rayuwa masu inganci, da raya fasahohin zamani da sauransu, wadanda dukkanin su ke zama muhimmin misali mai kima ga sauran kasashe masu tasowa musamman na Afirka.

 

Kasashen Afirka na iya koyi da dabarun kasar Sin ta fuskar aiwatar da managartan manufofin raya kai, da gudanar da sauye-sauye da zamanantarwa, ta yadda su ma za su daga matsayin su daga kasashen da alummun suke fama da karancin karfin tattalin arziki zuwa cibiyoyin raya tattalin arziki a matakin kasa da kasa.

  • Xi Ya Mika Gaisuwar Ban Girma Ga Dattawa A Jajibirin Ranar Tsofaffin Kasar Sin
  • Ban Yi Nadamar Yakar PDP A Zaben 2023 Ba – Wike

Mun dai ga misalan hakan a bangaren kasar Sin, wadda ta kawar da fatara, da cike gibi tsakanin mawadata da masu rauni, zuwa wanzar da ci gaba mai dorewa a dukkanin fannoni, matakan da suka kai kasar zuwa turbar samun ci gaba a dukkanin bangarori, da daidaita tafiya tsakanin raya tattalin arzikin kasa da ci gaban zamantakewa da walwalar alumma.

 

Labarai Masu Nasaba

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

A daya hannun, muna iya cewa yadda kasashen Afirka ke kara rungumar tafiyar samar da ci gaba tare da kasar Sin, karkashin tsare-tsare, da dandaloli daban daban abun a yaba ne. A duk inda muka duba muna iya ganin ayyukan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na raba ababen more rayuwa, da musayar kwarewa, da musayar aladu, da karfafa kawance, da bunkasa cinikayyar hajoji da hidimomi tsakanin sassan biyu.

 

Baya ga hakan, wasu karin sassa da ya kamata sassan biyu su inganta hadin gwiwa su ne batun samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kare muhallin halittu, da rage tasirin dumamar yanayi, da raya samar da makamashi mai tsafta, fannonin da tuni kasar Sin ta yi nisa a fannin cimma nasarar su.

 

Yayin da ake duba yiwuwar fadada kawance, da cudanya tsakanin Sin da kasashen Afirka a dukkanin fannoni, wajibi ne a jinjinawa yadda Sin din ke fadada tallafin da take baiwa kasashen Afirka ta fuskoki da dama, kamar samar da yankunan raya masanaantu, da yankunan cinikayya maras shinge, da taimakon raya fasahohin noma na zamani da dai sauran su.

 

Kaza lika, ya zama dole a yabawa kasar Sin don gane da sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa 10 da ta gabatar a baya bayan nan, don ingiza zamanantar da kasashen Afirka abokan tafiyarta, shirye-shiryen da ko shakka babu za su yaukaka dunkulewar ayyukan hadin kan sassan biyu, kana sun dace da ajandar raya nahiyar Afirka ta nan zuwa shekarar 2063, da ma ajandar raya yankin cinikayya maras shinge na daukacin kasahen Afirka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Next Post

Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

Related

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

17 minutes ago
Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

17 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

18 hours ago
Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba
Daga Birnin Sin

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

19 hours ago
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

20 hours ago
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

21 hours ago
Next Post
Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

LABARAI MASU NASABA

majalisar kasa

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

July 25, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

July 25, 2025
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

July 25, 2025
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

July 25, 2025
Amcon

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

July 25, 2025
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.