• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Hanyoyin Tabbatar Da Tsaro A Duniya Da Inganta Amincewa Da Juna A Taron Dandalin Tsaro Na Xiangshan 

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Samar Da Hanyoyin Tabbatar Da Tsaro A Duniya Da Inganta Amincewa Da Juna A Taron Dandalin Tsaro Na Xiangshan 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa la’akari da batutuwan tsaro da dama da duniya ke fuskanta, taron dandalin Xiangshan na birnin Beijing na kasar Sin karo na 10 ya kasance daya daga cikin muhimman tarukan tsara manufofin tsaro tare a duk duniya. A bana, mahalarta taron za su yi zama a nan birnin Beijing, domin tattauna batutuwan farko dake fuskantar tsaron kasashen duniya.

 

Yaki da kalubalen tsaro da ke kunno kai daga wurare da lokutan da ba a yi hasashensu ba, na iya taimakawa wajen hada kan masu ruwa da tsaki a kan manufa daya, yayin da suke da ikon yin hadin gwiwa yadda ya kamata kan wadannan matsalolin da suke gurgunta ci gaban kasashen duniya musamman kasashe masu tasowa. Duk da haka, wannan dandalin tsaro zai bankado cikakkun matakan tsaro don inganta zaman lafiya da bunkasuwa, da wadata ga dukkanin kasashe. Da tabbatar da duniyar zaman lafiya da kwanciyar hankali mai amfanar dukkan al’ummomi.

  • Xi Ya Jaddada Bukatar Karfafawa Mata Gwiwa Domin Bayar Da Gudunmowarsu Ga Zamanantar Da Kasar Sin
  • Hun Manet: Kasar Kambodiya Na Goyon Bayan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Tun kafuwar dandalin a shekara ta 2006, dandalin tsaro na Xiangshan na Beijing, wanda ke kiyaye ka’idojin “Daidaito, Bude kofofi, Hadin kai, musayar ra’ayoyi”, ya zama wani muhimmin dandalin tsaro na kasa da kasa. Dandalin yana daga cikin manyan tarukan tattaunawa kan manufofin tsaro na kasa da kasa a duniya, ta hanyar bude kafar tattaunawa don magance batutuwan da suka shafi tsaro na duniya, da habaka hadin gwiwa, da karfafa amincewar juna. Har ila yau, yana baiwa kasashe masu tasowa damar bayyana ra’ayoyinsu da kuma shiga harkokin tafiyar da harkokin tsaron duniya. Kasar Sin ta dauki nauyin dandalin ne domin inganta ra’ayoyinta kan muhimman batutuwan tsaro na kasa da kasa da na shiyya-shiyya, da shirya tattaunawa da jami’an mahalarta taron.

Taron dandalin na bana, mai taken “Tsaro na bai daya, zaman lafiya mai dorewa” ya mai da hankali kan shawarar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen duniya kan batun tsaro, yana baiwa dukkanin bangarori damar bayyana ra’ayoyinsu bisa daidato da adalci. Har ila yau, ana tattauna matsalolin tsaro, da bin hanyoyin samar da tsaro, da inganta hadin gwiwar tsaro. Za a gudanar da tarukan musamman guda takwas a lokaci guda da kuma zama hudu a dandalin na bana. Haka kuma, za a gudanar da turakan karawa juna sani a fannonin tsaro daban-daban musamman taron karawa juna sani na jami’an tsaro matasa da malamai masana harkokin tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Taron na dandalin tattaunawa na Xiangshan na Beijin karo na 10 dake gudana daga ranar 29 zuwa ranar 31 ga watan Oktoba ya hada tawagogin hukuma daga kasashe sama da 90 da kungiyoyin kasa da kasa, gami da wakilai 22 a matakin ministan tsaro ko sama da haka, da wakilai 14 a matakin hafsan soji. Kana, fiye da masana 200 daga kasashe da yankuna sama da 50 sun nemi shiga dandalin. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Yan Fashin Daji Suka Yi Awon Gaba Da Kawayen Amarya A Katsina

Next Post

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Amfanawa Al’ummar Nijeriya

Related

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

1 hour ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

2 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

3 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

4 hours ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

6 hours ago
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

1 day ago
Next Post
Ziri daya

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Amfanawa Al’ummar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.