ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Hanyoyin Tabbatar Da Tsaro A Duniya Da Inganta Amincewa Da Juna A Taron Dandalin Tsaro Na Xiangshan 

by CGTN Hausa
3 years ago
Xiangshan

Bisa la’akari da batutuwan tsaro da dama da duniya ke fuskanta, taron dandalin Xiangshan na birnin Beijing na kasar Sin karo na 10 ya kasance daya daga cikin muhimman tarukan tsara manufofin tsaro tare a duk duniya. A bana, mahalarta taron za su yi zama a nan birnin Beijing, domin tattauna batutuwan farko dake fuskantar tsaron kasashen duniya.

 

Yaki da kalubalen tsaro da ke kunno kai daga wurare da lokutan da ba a yi hasashensu ba, na iya taimakawa wajen hada kan masu ruwa da tsaki a kan manufa daya, yayin da suke da ikon yin hadin gwiwa yadda ya kamata kan wadannan matsalolin da suke gurgunta ci gaban kasashen duniya musamman kasashe masu tasowa. Duk da haka, wannan dandalin tsaro zai bankado cikakkun matakan tsaro don inganta zaman lafiya da bunkasuwa, da wadata ga dukkanin kasashe. Da tabbatar da duniyar zaman lafiya da kwanciyar hankali mai amfanar dukkan al’ummomi.

ADVERTISEMENT
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Karfafawa Mata Gwiwa Domin Bayar Da Gudunmowarsu Ga Zamanantar Da Kasar Sin
  • Hun Manet: Kasar Kambodiya Na Goyon Bayan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Tun kafuwar dandalin a shekara ta 2006, dandalin tsaro na Xiangshan na Beijing, wanda ke kiyaye ka’idojin “Daidaito, Bude kofofi, Hadin kai, musayar ra’ayoyi”, ya zama wani muhimmin dandalin tsaro na kasa da kasa. Dandalin yana daga cikin manyan tarukan tattaunawa kan manufofin tsaro na kasa da kasa a duniya, ta hanyar bude kafar tattaunawa don magance batutuwan da suka shafi tsaro na duniya, da habaka hadin gwiwa, da karfafa amincewar juna. Har ila yau, yana baiwa kasashe masu tasowa damar bayyana ra’ayoyinsu da kuma shiga harkokin tafiyar da harkokin tsaron duniya. Kasar Sin ta dauki nauyin dandalin ne domin inganta ra’ayoyinta kan muhimman batutuwan tsaro na kasa da kasa da na shiyya-shiyya, da shirya tattaunawa da jami’an mahalarta taron.

Taron dandalin na bana, mai taken “Tsaro na bai daya, zaman lafiya mai dorewa” ya mai da hankali kan shawarar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen duniya kan batun tsaro, yana baiwa dukkanin bangarori damar bayyana ra’ayoyinsu bisa daidato da adalci. Har ila yau, ana tattauna matsalolin tsaro, da bin hanyoyin samar da tsaro, da inganta hadin gwiwar tsaro. Za a gudanar da tarukan musamman guda takwas a lokaci guda da kuma zama hudu a dandalin na bana. Haka kuma, za a gudanar da turakan karawa juna sani a fannonin tsaro daban-daban musamman taron karawa juna sani na jami’an tsaro matasa da malamai masana harkokin tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Taron na dandalin tattaunawa na Xiangshan na Beijin karo na 10 dake gudana daga ranar 29 zuwa ranar 31 ga watan Oktoba ya hada tawagogin hukuma daga kasashe sama da 90 da kungiyoyin kasa da kasa, gami da wakilai 22 a matakin ministan tsaro ko sama da haka, da wakilai 14 a matakin hafsan soji. Kana, fiye da masana 200 daga kasashe da yankuna sama da 50 sun nemi shiga dandalin. (Muhammed Yahaya)

Xiangshan
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Next Post
Ziri daya

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Amfanawa Al’ummar Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.