• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Kyakkyawar Makoma Ga Yaran Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Nazari
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gabata ne aka gudanar da bikin ranar yara ta duniya. Rana ce da aka ware don jawo hankalin al’umma a kan halin da yaran Nijeriya ke ciki, musamman ganin dukanmu mun taba kasance wa yara a wani lokaci na rayuwarmu.

 

Biki ne da ke da matukar muhimmanci don yana tunatar da mu bukatar kula tare da samar da kariya ta musamman ga yara don ta haka ne za mu tabbatar da rayuwamu data al’ummar da za ta biyo bayanmu ta wanzu. Rana ce da ake bikin yara kanana da basu san komai ba, rana ce ta tabbatar da hakokinsu da kuma jinjina gudummawarsu ga tsayuwar gida da al’umma gaba daya.

  • Za A Rika Tuna Wa Da Mijina A Matsayin Gwarzon Gina Rayuwar Matasa –Aisha Buhari

Ra’ayin wannan jarida shi ne a daidai lokacin da muke bikin ranar yara ta duniya bai kamata mu manta abin da ya shafi kula da jin dadin rayuwar su yaran ba. Idan za a iya tunawa ‘yan shekarun nan ne aka samu karuwar yara da suke garanranba a kan titunan kasar nan ba tare da suna zuwa makaranta ba, wannan kuma abu ne mai matukar tayar da hankali.

Abu ne mai tayar da hankali a halin yanzu yadda yawan yara marasa zuwa makaranta a Nijeriya ke karuwa. Wani rahoton da aka gudanar a kwanan-kwanan nan ya nuna cewa, yara marasa zuwa makaranta ya karu daga yara Miliyan 10.5 zua yara miliyan 18.5 a shekarar 2022. Wannan wata babbar barazana ce ga rayuwar kasar nan gaba daya, wanda hakan yana kawo tarnaki da ci gaban kasa yana kuma kara talauci a tsakanin al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

Abin lura kuma a nan shi ne yawan yaran da ke garanramba basa zuwa makaranta a Nijeriya sun fi yawan al’ummar kasar Norway, Singapore da Cuba. Wannan abin kunya ne kuma bai kamata a bari ya ci gaba da yin haka ba.

A kasar da al’amurran ‘yan ta’adda ya addaba, ‘yan bindiga a yankin arewa ta yamma da arewa ta gabas da kuma yanklin arewa ta tsakiya, yaran da basa zuwa makartanta da ke yawo a titunan kasar nan na iya zama wajewn da ‘yan ta’adda za su samu kayan aiki.

A bayyane abin yake cewa, ilimi shi ne makullin samun ci gaba a rayuwa ta hanyar bsamun ilimi ne ake samun ci gaba da walwala a harkokin yau da kullum. Saboda haka kange yaranmu daga samun cikakke kuma ingantaccen ilimi ba wai dakile hakkin yaran ba ne kadai amma hakan yana kuma nuna tamkar kawo cikas ga ci gaban kasa baki daya.

Muna bayar da shawarar cewa, yakamata gwamnatoci a dukkan matakai su yi maganin matsalolin da shuka shafi talauci bambanci a tsakanin mata da maza da kuma dukkan matsalolin da ke kawo wa cikas a harkokin rayuwarsu.

A ‘yan shekarun da suka gabata Nijeriya ta ga abubuwan tayar da hankali a kana bin da shuka shafi rayuwar yara, kamar sace ‘yan makarantar Chibok da kisan da yarinya Leah Sharibu, da kuma sauran yaran da suka fada hannun ‘yan ta’adda a lokutta daban-daban a fadin tarayyar Nijeriya.

Rahoton Kungiyar Kare Hakkin Dan’adam ya nuna cewa, tun da aka sace ‘yan mata 276 da ‘yan Boko Haram suka yi a makarantar Chibok, zuwa yanzu ‘yan bindiga sun sace yara fiye da 1,500 a makarantu daban daban.
Wadannan ayyukan ta’addanci ba wai yana tayar da hankullan wadanda abin ya shafa kawai ba ne, yana sanya tsoro da razana a cikin zukatan al’umma a sassan Nijeriya.

A kan haka yakamata wadanan su zaburar da gwamnati a kan bukatar samar da cikakken tsaro ga yaranmu a dukkan makarantun tarayyar kasar nan.

Kowanne yaro yana da hakkin ya yi karatu a yanayi mai aminci tare da samar masa da cikakken tsaro. Ya kamata hukuma ta kara kaimi don ganin ba a kai ga sake sace yara a makarantu ba. Tabbatar da haka kuma yana bukatar hadin kai a tsakanin rundunonin tsaronmu, ta yadda za a dakile shirin da suke a kowanne lokaci na kai hari ga makarantunmu.

Hukumar Majalisar Dinkin Duniya ta UNICEF ta bayar da rahoton cewa, Nijeriya ne ke dauke da mafi yawan yara kanana da aka yi wa aure tun kafin su kosa, rahoton ya kara da cewa, yara ‘yan mata fiye da miliyan 23 ake aurarwa tun suna kanana a Nijeriya.

Idan za a iya tunawa Nijeriya ta sanya hannu a kan dokar kare hakkin yara ta 2023, a halin yanzu kuma jihohi 34 daga cikin jihohi 36 da muke da su suka sanya hannu a kan doka a jihohinsu wanda aka yi maganar ci da gumin yara, yi musu aure da wuri da auren dole.

A ra’ayinmu, matsalolin da ke fuskantar yara na bukatar a hada hannu don kawo karshensa, lamarin ya kuma fara ne da gwamnati, yakamata gwamnati ta samar da issasun kudi da abubuwan da ake bukata wajen samar da ingantaccen ilimi ga yara a dukkan matakai. Da kuma bukatar zuba jari don gyara tare da gina sabbin azuzuwa don yaranmu su samu yanayin da za su yi karatu ba tare da wata tsangwam ba.

A yayin bikin ranar yara a Nijeriya, ya kamata mu kara fahimtar matsalolin da ke hana ruwa gudu wajen samar wa yaranmu rayuwa ta gari, hakan kuma ke haifar da yawan yaran da basa zuwa makaranta sai yawon bara, ya kamata a gaggauta daukar matakin ganin samar da yanayin da yaranmu za su yi karatu a tsanake ba tare da matsala ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Mu Yi Gaggawar Cire Tallafin Mai Ko Ya Halaka ‘Yan Nijeriya – Shettima

Next Post

Maganar Gwamnan Zamfara Dauda Ya Mallaki Tiriliyan 9 Ba Gaskiya Ba Ne Bata Da Tushe

Related

Mataimakin shugaban kasa
Nazari

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

5 days ago
haraji
Nazari

Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

1 month ago
Nijeriya
Nazari

Shirin Fim Kan Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Kan Turbar Dimokuradiyya: Tasiri Da Muhimmanci

3 months ago
Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya
Nazari

Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya

8 months ago
Sinadarin Ƙara Kuzari Lokacin Jima’i
Nazari

Sinadarin Ƙara Kuzari Lokacin Jima’i

12 months ago
Nijeriya
Labarai

Farashin Shinkafa, Tumatir Da Gari Ya Qaru Da Kashi 141 Cikin Shekara Guda – NBS

1 year ago
Next Post
Maganar Gwamnan Zamfara Dauda Ya Mallaki Tiriliyan 9 Ba Gaskiya Ba Ne Bata Da Tushe

Maganar Gwamnan Zamfara Dauda Ya Mallaki Tiriliyan 9 Ba Gaskiya Ba Ne Bata Da Tushe

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.