ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Rika Tuna Wa Da Mijina A Matsayin Gwarzon Gina Rayuwar Matasa –Aisha Buhari

by Sadiq
3 years ago
Aisha Buhari

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta ce za a tuna da mijinta, shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin shugaban kasa wanda ya bai wa matasa fifiko.

Da ta ke jawabi a Abuja ranar Talata lokacin da ta kaddamar da shirin Health Initiative for Rural Dwellers (HIRD), ta ce shugaban ya fi sha’awar goyon bayan ga shirin gina matasa.

  • Inter Milan Ta Je Wasan Karshe Na Gasar Zakarun Turai
  • Hukumar NDLEA Ta Cafke Mutane 85 Kan Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Gidan Casu A Kano

“Za a tuna da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin wacce ke ba da fifiko ga ci gaban matasa.

ADVERTISEMENT

“Shugaban kasa yana da kishin NYSC. Goyon bayansa ga wannan tsari ya dogara ne a kan imaninsa ga Nijeriya raya, da kuma godiya ga gudummawar wadannan matasa maza da mata. Don haka, iyalina a kodayaushe suna yi wa ’yan uwa masu hidimar kasa da ke aiki a Daura, Jihar Katsina, zuwa liyafar shugaban kasa a lokacin bukukuwan Sallah,” in ji shi.

Ta kuma yi kira ga masu gudanar da wannan tsari na NYSC da kuma ’yan kungiyar da kada su yi kasa a gwiwa wajen inganta hadin kan kasa ta hanyar samar da ingantacciyar hidima ga al’umma ba tare da la’akari da jiha ko wurin aiki ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Buhari ta bayyana cewa an samu nasarar bullo da shirin (HIRD), don haka ofishinta ya yaba da aikin ta hanyar bayar da gudummawar “kayan aikin asibitin tafi da gidanka ga shirin domin bunkasa nasarar kungiyar likitoci.”

Ta ce shirin ya yi tasiri matuka musamman a tsakanin mazauna karkara, wanda ke ci gaba da samun yabo daga ciki da wajen kasar nan.

A nasa bangaren, Darakta Janar na masu yi wa kasa hidima (NYSC) Birgediya Janar Yushau Dogara Ahmed ya ce shirin na HIRD ya samo asali ne daga bukatar magance matsalolin kiwon lafiya da ke addabar talakawa a yankunan karkara a fadin kasar nan.

Ya ce shirin wanda aka fara shi a shekarar 2014, wani dandali ne da jami’an kiwon lafiya da suka hada da likitoci, masu hada magunguna, ma’aikatan jinya, da likitocin hakori, da dai sauransu, suke ba da kiwon lafiya kyauta ga jama’a, musamman talakawan karkara.

Ahmed ya ruwaito cewa kawo yanzu sama da ‘yan Nijeriya miliyan uku ne suka ci gajiyar shirin.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

'Yan Bindiga Sun Kashe Ma'aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.