ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Rika Tuna Wa Da Mijina A Matsayin Gwarzon Gina Rayuwar Matasa –Aisha Buhari

by Sadiq
3 years ago
Aisha Buhari

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta ce za a tuna da mijinta, shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin shugaban kasa wanda ya bai wa matasa fifiko.

Da ta ke jawabi a Abuja ranar Talata lokacin da ta kaddamar da shirin Health Initiative for Rural Dwellers (HIRD), ta ce shugaban ya fi sha’awar goyon bayan ga shirin gina matasa.

  • Inter Milan Ta Je Wasan Karshe Na Gasar Zakarun Turai
  • Hukumar NDLEA Ta Cafke Mutane 85 Kan Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Gidan Casu A Kano

“Za a tuna da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin wacce ke ba da fifiko ga ci gaban matasa.

ADVERTISEMENT

“Shugaban kasa yana da kishin NYSC. Goyon bayansa ga wannan tsari ya dogara ne a kan imaninsa ga Nijeriya raya, da kuma godiya ga gudummawar wadannan matasa maza da mata. Don haka, iyalina a kodayaushe suna yi wa ’yan uwa masu hidimar kasa da ke aiki a Daura, Jihar Katsina, zuwa liyafar shugaban kasa a lokacin bukukuwan Sallah,” in ji shi.

Ta kuma yi kira ga masu gudanar da wannan tsari na NYSC da kuma ’yan kungiyar da kada su yi kasa a gwiwa wajen inganta hadin kan kasa ta hanyar samar da ingantacciyar hidima ga al’umma ba tare da la’akari da jiha ko wurin aiki ba.

LABARAI MASU NASABA

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Buhari ta bayyana cewa an samu nasarar bullo da shirin (HIRD), don haka ofishinta ya yaba da aikin ta hanyar bayar da gudummawar “kayan aikin asibitin tafi da gidanka ga shirin domin bunkasa nasarar kungiyar likitoci.”

Ta ce shirin ya yi tasiri matuka musamman a tsakanin mazauna karkara, wanda ke ci gaba da samun yabo daga ciki da wajen kasar nan.

A nasa bangaren, Darakta Janar na masu yi wa kasa hidima (NYSC) Birgediya Janar Yushau Dogara Ahmed ya ce shirin na HIRD ya samo asali ne daga bukatar magance matsalolin kiwon lafiya da ke addabar talakawa a yankunan karkara a fadin kasar nan.

Ya ce shirin wanda aka fara shi a shekarar 2014, wani dandali ne da jami’an kiwon lafiya da suka hada da likitoci, masu hada magunguna, ma’aikatan jinya, da likitocin hakori, da dai sauransu, suke ba da kiwon lafiya kyauta ga jama’a, musamman talakawan karkara.

Ahmed ya ruwaito cewa kawo yanzu sama da ‘yan Nijeriya miliyan uku ne suka ci gajiyar shirin.

MASU ALAKA

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi
Manyan Labarai

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

'Yan Bindiga Sun Kashe Ma'aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.