• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samuel Eto’o Na Fuskantar Zarge-zarge A Kamaru

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Kamaru

Wasu lauyoyin tsohon dan wasan Kamaru, Samuel Eto’o, wanda kuma shi ne shugaban hukumar kwallon kafar kasar, sun musanta cewar an sanar da matakan shari’a a kansa.

A wani jawabi daga kamfanin lauyoyin Faransa, Bey & Associes ya yi watsi da zargin da aka yi wa fitaccen tsohon dan kwallon mai shekara 42 da cewar ”Batun zai shafi bata suna”.

  • Kazakhstan, Kasa Marar Ruwa Mafi Girma A Duniya, Tana Da Nata Hanyar Shiga Teku
  • Gajiya Ce Ta Sa Na Fadi Yayin Tantance Ni A Majalisa — Balarabe

Ya kara da cewar ba a sanar da Eto’o ba cewar an dauki wani mataki ko sanar da shi abin da ya shafi shari’a tun da a ranar Juma’a aka zargi dan wasan da cewar yana fuskantar mataki na shari’a da ya shafi cogen wasa da cewar ‘yansandan Kamaru na tare da takardun da ake zarginsa da yin amfani da matsayinsa domin amfanin kai da cin hanci da wasu zarge-zarge da dama.

Wannan ba shi ne karon farko da Eto’o ke fuskanta kalubale irin haka ba inda ko a makon jiya, wani rukunin mahukuntan wasanni a Kamaru ya aike da budaddiyar wasika ga hukumar kwallon kafa ta duniya, FIFA, kan cewar hukumar kwallon kafa ta duniya ta yi gum, duk da tuhume-tumumen da ake yi wa Eto’o da wasu mukarrabansa a hukumar kwallon kafar kasar.

Wadanda suka sa hannu kan wasikar sun hada da babban mamba a kwamitin Fecafoot, Guibai Gatama da mataimakin shugaban kwararrun ‘yan kwallon kafar Kamaru, wadanda ke gabatar da babbar gasar kwallon kafa ta kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

An yi zargin cewar tsohon dan wasan na Barcelona da Inter Milan da Chelsea yana tursasa kansa ta hanyar da ba ta dace ba a kujerar shugaban kwallon kafar kasar (Fecafoot).

Wasikar ta kara da cewar lamarin ya zama mai muhimmanci fiye da wanda ya shafi shugaban hukumar kwallon kafar Sifaniya, Luis Rubiales da ‘yar wasa Jenni Hermoso, inda ta kai FIFA ta dakatar da Rubiales kwana 90 da tsara hanyar da aka dauka don ladabtar da shi.

Lokacin da yake mayar da martani kan wasikar kamfanin lauyoyi na Bey & Associes ya ce Eto’o ya yi tsare-tsare da yawa don sauya alkiblar hukumar kwallon kafar Kamaru da gudanar da mulkin da masu ruwa da tsaki suka mara wa baya.

Sun kuma kira wasikar da cewar mai hadari da bata suna, ya kara da cewar Eto’o ya bugi kirjin tsari da zai kawo karshen wasu daidaiku, wadanda koda yaushe a shirye suke su yi duk abin da zai sa kada su rasa cin hanci da rashawa da suke karba.

A watan Yuni, wani rukunin kungiyoyi ‘yan dagaji da ake kira Amateur clubs a Kamaru suka yi kira da Eto’o ya yi murabus da cewar ya kawo rashin bin tsari, inda suka kada kuri’a da mutum 11-1 suka bukaci da ya kara gaba.

A watan Agusta hukumar kwallon kafar Afirka, Caf ta fara wani bincike kan zargin da ake yi wa Eto’o da cewar ta karbi wasiku daga bangaren masu ruwa da tsaki a kwallon kafar Kamaru, za kuma ta duba dukkan korafin kan doka da ca’ar CAF.

Jawabin na CAF ya kara da cewar zargin yana da girma, amma Eto bai da laifi har sai wata kotu ta tabbar da zargin da ake yi masa.

Lokacin da Eto’o ke kan ganiya an nada shi fitatcen dan kwallon Afirka karo hudu, wanda ya lashe Champions League uku da buga wa Kamaru wasa 115 da lashe kofin nahiyar Afirka biyu tare da kasar wadda ake kira “Indomitable Lions”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Next Post
Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.