• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samuel Eto’o Na Fuskantar Zarge-zarge A Kamaru

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Samuel Eto’o Na Fuskantar Zarge-zarge A Kamaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu lauyoyin tsohon dan wasan Kamaru, Samuel Eto’o, wanda kuma shi ne shugaban hukumar kwallon kafar kasar, sun musanta cewar an sanar da matakan shari’a a kansa.

A wani jawabi daga kamfanin lauyoyin Faransa, Bey & Associes ya yi watsi da zargin da aka yi wa fitaccen tsohon dan kwallon mai shekara 42 da cewar ”Batun zai shafi bata suna”.

  • Kazakhstan, Kasa Marar Ruwa Mafi Girma A Duniya, Tana Da Nata Hanyar Shiga Teku
  • Gajiya Ce Ta Sa Na Fadi Yayin Tantance Ni A Majalisa — Balarabe

Ya kara da cewar ba a sanar da Eto’o ba cewar an dauki wani mataki ko sanar da shi abin da ya shafi shari’a tun da a ranar Juma’a aka zargi dan wasan da cewar yana fuskantar mataki na shari’a da ya shafi cogen wasa da cewar ‘yansandan Kamaru na tare da takardun da ake zarginsa da yin amfani da matsayinsa domin amfanin kai da cin hanci da wasu zarge-zarge da dama.

Wannan ba shi ne karon farko da Eto’o ke fuskanta kalubale irin haka ba inda ko a makon jiya, wani rukunin mahukuntan wasanni a Kamaru ya aike da budaddiyar wasika ga hukumar kwallon kafa ta duniya, FIFA, kan cewar hukumar kwallon kafa ta duniya ta yi gum, duk da tuhume-tumumen da ake yi wa Eto’o da wasu mukarrabansa a hukumar kwallon kafar kasar.

Wadanda suka sa hannu kan wasikar sun hada da babban mamba a kwamitin Fecafoot, Guibai Gatama da mataimakin shugaban kwararrun ‘yan kwallon kafar Kamaru, wadanda ke gabatar da babbar gasar kwallon kafa ta kasar.

Labarai Masu Nasaba

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

An yi zargin cewar tsohon dan wasan na Barcelona da Inter Milan da Chelsea yana tursasa kansa ta hanyar da ba ta dace ba a kujerar shugaban kwallon kafar kasar (Fecafoot).

Wasikar ta kara da cewar lamarin ya zama mai muhimmanci fiye da wanda ya shafi shugaban hukumar kwallon kafar Sifaniya, Luis Rubiales da ‘yar wasa Jenni Hermoso, inda ta kai FIFA ta dakatar da Rubiales kwana 90 da tsara hanyar da aka dauka don ladabtar da shi.

Lokacin da yake mayar da martani kan wasikar kamfanin lauyoyi na Bey & Associes ya ce Eto’o ya yi tsare-tsare da yawa don sauya alkiblar hukumar kwallon kafar Kamaru da gudanar da mulkin da masu ruwa da tsaki suka mara wa baya.

Sun kuma kira wasikar da cewar mai hadari da bata suna, ya kara da cewar Eto’o ya bugi kirjin tsari da zai kawo karshen wasu daidaiku, wadanda koda yaushe a shirye suke su yi duk abin da zai sa kada su rasa cin hanci da rashawa da suke karba.

A watan Yuni, wani rukunin kungiyoyi ‘yan dagaji da ake kira Amateur clubs a Kamaru suka yi kira da Eto’o ya yi murabus da cewar ya kawo rashin bin tsari, inda suka kada kuri’a da mutum 11-1 suka bukaci da ya kara gaba.

A watan Agusta hukumar kwallon kafar Afirka, Caf ta fara wani bincike kan zargin da ake yi wa Eto’o da cewar ta karbi wasiku daga bangaren masu ruwa da tsaki a kwallon kafar Kamaru, za kuma ta duba dukkan korafin kan doka da ca’ar CAF.

Jawabin na CAF ya kara da cewar zargin yana da girma, amma Eto bai da laifi har sai wata kotu ta tabbar da zargin da ake yi masa.

Lokacin da Eto’o ke kan ganiya an nada shi fitatcen dan kwallon Afirka karo hudu, wanda ya lashe Champions League uku da buga wa Kamaru wasa 115 da lashe kofin nahiyar Afirka biyu tare da kasar wadda ake kira “Indomitable Lions”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yancin Kai: Manyan Matsalolin Da Suka Zame Wa Nijeriya Kashin Bakin Tulu

Next Post

Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

Related

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds
Wasanni

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

9 hours ago
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya
Wasanni

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

14 hours ago
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa
Wasanni

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

3 days ago
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City
Wasanni

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

4 days ago
Boniface
Wasanni

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

6 days ago
Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong
Wasanni

Ronaldo Ya Samu Kyakkyawar Tarba A Hong Kong

1 week ago
Next Post
Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.