ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samuel Eto’o Na Fuskantar Zarge-zarge A Kamaru

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kamaru

Wasu lauyoyin tsohon dan wasan Kamaru, Samuel Eto’o, wanda kuma shi ne shugaban hukumar kwallon kafar kasar, sun musanta cewar an sanar da matakan shari’a a kansa.

A wani jawabi daga kamfanin lauyoyin Faransa, Bey & Associes ya yi watsi da zargin da aka yi wa fitaccen tsohon dan kwallon mai shekara 42 da cewar ”Batun zai shafi bata suna”.

  • Kazakhstan, Kasa Marar Ruwa Mafi Girma A Duniya, Tana Da Nata Hanyar Shiga Teku
  • Gajiya Ce Ta Sa Na Fadi Yayin Tantance Ni A Majalisa — Balarabe

Ya kara da cewar ba a sanar da Eto’o ba cewar an dauki wani mataki ko sanar da shi abin da ya shafi shari’a tun da a ranar Juma’a aka zargi dan wasan da cewar yana fuskantar mataki na shari’a da ya shafi cogen wasa da cewar ‘yansandan Kamaru na tare da takardun da ake zarginsa da yin amfani da matsayinsa domin amfanin kai da cin hanci da wasu zarge-zarge da dama.

ADVERTISEMENT

Wannan ba shi ne karon farko da Eto’o ke fuskanta kalubale irin haka ba inda ko a makon jiya, wani rukunin mahukuntan wasanni a Kamaru ya aike da budaddiyar wasika ga hukumar kwallon kafa ta duniya, FIFA, kan cewar hukumar kwallon kafa ta duniya ta yi gum, duk da tuhume-tumumen da ake yi wa Eto’o da wasu mukarrabansa a hukumar kwallon kafar kasar.

Wadanda suka sa hannu kan wasikar sun hada da babban mamba a kwamitin Fecafoot, Guibai Gatama da mataimakin shugaban kwararrun ‘yan kwallon kafar Kamaru, wadanda ke gabatar da babbar gasar kwallon kafa ta kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

An yi zargin cewar tsohon dan wasan na Barcelona da Inter Milan da Chelsea yana tursasa kansa ta hanyar da ba ta dace ba a kujerar shugaban kwallon kafar kasar (Fecafoot).

Wasikar ta kara da cewar lamarin ya zama mai muhimmanci fiye da wanda ya shafi shugaban hukumar kwallon kafar Sifaniya, Luis Rubiales da ‘yar wasa Jenni Hermoso, inda ta kai FIFA ta dakatar da Rubiales kwana 90 da tsara hanyar da aka dauka don ladabtar da shi.

Lokacin da yake mayar da martani kan wasikar kamfanin lauyoyi na Bey & Associes ya ce Eto’o ya yi tsare-tsare da yawa don sauya alkiblar hukumar kwallon kafar Kamaru da gudanar da mulkin da masu ruwa da tsaki suka mara wa baya.

Sun kuma kira wasikar da cewar mai hadari da bata suna, ya kara da cewar Eto’o ya bugi kirjin tsari da zai kawo karshen wasu daidaiku, wadanda koda yaushe a shirye suke su yi duk abin da zai sa kada su rasa cin hanci da rashawa da suke karba.

A watan Yuni, wani rukunin kungiyoyi ‘yan dagaji da ake kira Amateur clubs a Kamaru suka yi kira da Eto’o ya yi murabus da cewar ya kawo rashin bin tsari, inda suka kada kuri’a da mutum 11-1 suka bukaci da ya kara gaba.

A watan Agusta hukumar kwallon kafar Afirka, Caf ta fara wani bincike kan zargin da ake yi wa Eto’o da cewar ta karbi wasiku daga bangaren masu ruwa da tsaki a kwallon kafar Kamaru, za kuma ta duba dukkan korafin kan doka da ca’ar CAF.

Jawabin na CAF ya kara da cewar zargin yana da girma, amma Eto bai da laifi har sai wata kotu ta tabbar da zargin da ake yi masa.

Lokacin da Eto’o ke kan ganiya an nada shi fitatcen dan kwallon Afirka karo hudu, wanda ya lashe Champions League uku da buga wa Kamaru wasa 115 da lashe kofin nahiyar Afirka biyu tare da kasar wadda ake kira “Indomitable Lions”.

Kamaru
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
Wasanni

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
Wasanni

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
Wasanni

Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City

June 12, 2026
Next Post
Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.