ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samuel Eto’o Na Fuskantar Zarge-zarge A Kamaru

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Kamaru

Wasu lauyoyin tsohon dan wasan Kamaru, Samuel Eto’o, wanda kuma shi ne shugaban hukumar kwallon kafar kasar, sun musanta cewar an sanar da matakan shari’a a kansa.

A wani jawabi daga kamfanin lauyoyin Faransa, Bey & Associes ya yi watsi da zargin da aka yi wa fitaccen tsohon dan kwallon mai shekara 42 da cewar ”Batun zai shafi bata suna”.

  • Kazakhstan, Kasa Marar Ruwa Mafi Girma A Duniya, Tana Da Nata Hanyar Shiga Teku
  • Gajiya Ce Ta Sa Na Fadi Yayin Tantance Ni A Majalisa — Balarabe

Ya kara da cewar ba a sanar da Eto’o ba cewar an dauki wani mataki ko sanar da shi abin da ya shafi shari’a tun da a ranar Juma’a aka zargi dan wasan da cewar yana fuskantar mataki na shari’a da ya shafi cogen wasa da cewar ‘yansandan Kamaru na tare da takardun da ake zarginsa da yin amfani da matsayinsa domin amfanin kai da cin hanci da wasu zarge-zarge da dama.

ADVERTISEMENT

Wannan ba shi ne karon farko da Eto’o ke fuskanta kalubale irin haka ba inda ko a makon jiya, wani rukunin mahukuntan wasanni a Kamaru ya aike da budaddiyar wasika ga hukumar kwallon kafa ta duniya, FIFA, kan cewar hukumar kwallon kafa ta duniya ta yi gum, duk da tuhume-tumumen da ake yi wa Eto’o da wasu mukarrabansa a hukumar kwallon kafar kasar.

Wadanda suka sa hannu kan wasikar sun hada da babban mamba a kwamitin Fecafoot, Guibai Gatama da mataimakin shugaban kwararrun ‘yan kwallon kafar Kamaru, wadanda ke gabatar da babbar gasar kwallon kafa ta kasar.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

An yi zargin cewar tsohon dan wasan na Barcelona da Inter Milan da Chelsea yana tursasa kansa ta hanyar da ba ta dace ba a kujerar shugaban kwallon kafar kasar (Fecafoot).

Wasikar ta kara da cewar lamarin ya zama mai muhimmanci fiye da wanda ya shafi shugaban hukumar kwallon kafar Sifaniya, Luis Rubiales da ‘yar wasa Jenni Hermoso, inda ta kai FIFA ta dakatar da Rubiales kwana 90 da tsara hanyar da aka dauka don ladabtar da shi.

Lokacin da yake mayar da martani kan wasikar kamfanin lauyoyi na Bey & Associes ya ce Eto’o ya yi tsare-tsare da yawa don sauya alkiblar hukumar kwallon kafar Kamaru da gudanar da mulkin da masu ruwa da tsaki suka mara wa baya.

Sun kuma kira wasikar da cewar mai hadari da bata suna, ya kara da cewar Eto’o ya bugi kirjin tsari da zai kawo karshen wasu daidaiku, wadanda koda yaushe a shirye suke su yi duk abin da zai sa kada su rasa cin hanci da rashawa da suke karba.

A watan Yuni, wani rukunin kungiyoyi ‘yan dagaji da ake kira Amateur clubs a Kamaru suka yi kira da Eto’o ya yi murabus da cewar ya kawo rashin bin tsari, inda suka kada kuri’a da mutum 11-1 suka bukaci da ya kara gaba.

A watan Agusta hukumar kwallon kafar Afirka, Caf ta fara wani bincike kan zargin da ake yi wa Eto’o da cewar ta karbi wasiku daga bangaren masu ruwa da tsaki a kwallon kafar Kamaru, za kuma ta duba dukkan korafin kan doka da ca’ar CAF.

Jawabin na CAF ya kara da cewar zargin yana da girma, amma Eto bai da laifi har sai wata kotu ta tabbar da zargin da ake yi masa.

Lokacin da Eto’o ke kan ganiya an nada shi fitatcen dan kwallon Afirka karo hudu, wanda ya lashe Champions League uku da buga wa Kamaru wasa 115 da lashe kofin nahiyar Afirka biyu tare da kasar wadda ake kira “Indomitable Lions”.

Kamaru
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.