• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 5 ga watan Yuni ita ce ranar Muhalli ta Duniya. Ta hanyar kare muhalli ne kawai za mu iya kula da gidanmu wato duniyarmu, hakan ya kasance ra’ayi daya da dukkan bil Adama suka cimma. Ta yaya za a daidaita dangantakar dake tsakanin kiyaye muhalli da kuma ci gaban tattalin arziki da zamantakewa? Kasashen duniya suna binciko hanyoyi daban daban. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da manufar samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, wadda ta zama muhimmiyar ka’ida ga kasar Sin wajen kafa sabon tsarin ci gaba a sabon zamani.

Abin da ake kira “Samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba” a cikin kalaman Xi yana nufin cewa, bunkasuwar tattalin arziki bai dogara ne kan karuwar GDP kawai ba, dole ne a kula da dangantakar dake tsakanin bunkasuwar tattalin arziki da kuma kare muhalli yadda ya kamata, da kuma kafa ra’ayin cewa, kare yanayin muhalli shi ne kyautata karfin samar da kayayyaki, kyautata yanayin muhalli shi ne raya karfin samar da kayayyaki. Ba za a taba sadaukar da muhalli don samun ci gaban tattalin arziki na wucin gadi ba.

  • Sin Tana Son Yin Aiki Tare Da Hukumar IAEA Don Tabbatar Da Shawarar Ci Gaban Duniya Da Shawarar Tsaron Duniya
  • Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba A Bangaren Kyautata Muhallin Halittu

Alkaluma sun nuna cewa, fadin yankunan bishiyoyin da kasar Sin ta dasa ya zama na farko a duniya, kuma Sin kasa ce da ta fi saurin karuwar albarkatun gandun daji mafi yawa a duniya. Matsakaicin karuwar yawan makamashin da kasar Sin take amfani da shi a shekara-shekara ya kai 3%, amma matsakaicin karuwar tattalin arzikinta ya wuce 6% a kowace shekara, kuma yawan makamashin da take amfani ya ragu da 26.4%. Kasar Sin ta zama daya daga cikin kasashen da aka fi samun saurin raguwar makamashin da ake amfani da shi a duniya. A shekarar 2023, saurin karuwar wutar lantarki da kasar Sin ta samu daga makamashin da ake iya sabuntawa, alal misali hasken rana da iska, ya fi na baki dayan kasashen G7 yawa fiye da sau hudu, kuma ya ninka fiye da sau biyu idan aka kwatanta da na sauran kasashen duniya baki daya.

Achim Steiner, shugaban hukumar kula da shirin raya kasashe ta MDD wato UNDP, ya bayyana cewa, “Muna son samun ci gaba ba tare da fitar da yawan hayakin iskar Carbon mai dumama yanayi da kuma gurbata muhalli ba, wanda zai kunshi kowa. Kasar Sin ta baiwa kanta wata dama a wannan fannin, har ma ta ba duniya wata damar kara fahimtar yadda za a raya tattalin arzikin duniya ba tare da gurbata muhalli ba.”

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IAAMuhalliSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari’a Kan Rikicin Masarautar Kano

Next Post

Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

17 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

20 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.