• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Samun Bunkasuwa Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 5 ga watan Yuni ita ce ranar Muhalli ta Duniya. Ta hanyar kare muhalli ne kawai za mu iya kula da gidanmu wato duniyarmu, hakan ya kasance ra’ayi daya da dukkan bil Adama suka cimma. Ta yaya za a daidaita dangantakar dake tsakanin kiyaye muhalli da kuma ci gaban tattalin arziki da zamantakewa? Kasashen duniya suna binciko hanyoyi daban daban. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da manufar samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, wadda ta zama muhimmiyar ka’ida ga kasar Sin wajen kafa sabon tsarin ci gaba a sabon zamani.

Abin da ake kira “Samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba” a cikin kalaman Xi yana nufin cewa, bunkasuwar tattalin arziki bai dogara ne kan karuwar GDP kawai ba, dole ne a kula da dangantakar dake tsakanin bunkasuwar tattalin arziki da kuma kare muhalli yadda ya kamata, da kuma kafa ra’ayin cewa, kare yanayin muhalli shi ne kyautata karfin samar da kayayyaki, kyautata yanayin muhalli shi ne raya karfin samar da kayayyaki. Ba za a taba sadaukar da muhalli don samun ci gaban tattalin arziki na wucin gadi ba.

  • Sin Tana Son Yin Aiki Tare Da Hukumar IAEA Don Tabbatar Da Shawarar Ci Gaban Duniya Da Shawarar Tsaron Duniya
  • Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba A Bangaren Kyautata Muhallin Halittu

Alkaluma sun nuna cewa, fadin yankunan bishiyoyin da kasar Sin ta dasa ya zama na farko a duniya, kuma Sin kasa ce da ta fi saurin karuwar albarkatun gandun daji mafi yawa a duniya. Matsakaicin karuwar yawan makamashin da kasar Sin take amfani da shi a shekara-shekara ya kai 3%, amma matsakaicin karuwar tattalin arzikinta ya wuce 6% a kowace shekara, kuma yawan makamashin da take amfani ya ragu da 26.4%. Kasar Sin ta zama daya daga cikin kasashen da aka fi samun saurin raguwar makamashin da ake amfani da shi a duniya. A shekarar 2023, saurin karuwar wutar lantarki da kasar Sin ta samu daga makamashin da ake iya sabuntawa, alal misali hasken rana da iska, ya fi na baki dayan kasashen G7 yawa fiye da sau hudu, kuma ya ninka fiye da sau biyu idan aka kwatanta da na sauran kasashen duniya baki daya.

Achim Steiner, shugaban hukumar kula da shirin raya kasashe ta MDD wato UNDP, ya bayyana cewa, “Muna son samun ci gaba ba tare da fitar da yawan hayakin iskar Carbon mai dumama yanayi da kuma gurbata muhalli ba, wanda zai kunshi kowa. Kasar Sin ta baiwa kanta wata dama a wannan fannin, har ma ta ba duniya wata damar kara fahimtar yadda za a raya tattalin arzikin duniya ba tare da gurbata muhalli ba.”

 

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IAAMuhalliSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari’a Kan Rikicin Masarautar Kano

Next Post

Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

8 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

9 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

10 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

11 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

12 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

22 hours ago
Next Post
Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

Hajjin Bana: NDLEA Ta Kama Maniyyata Dauke da Hodar Iblis A Legas

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.