• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Ci Gaba Na Bukatar Hangen Nesa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Samun Ci Gaba Na Bukatar Hangen Nesa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Muhammad Buhari na Najeriya ya yi jawabi na musamman a jiya ranar Dimokuradiya, inda ya jaddada alkawarin tabbatar da tsaro a kasarsa. Kana a nasu bangare, jama’ar kasar sun ci gaba da nuna damuwa kan matsalolin rashin ayyukan yi, da tsadar rayuwa, a shafukan sada zumunta, inda suka bayyana koma bayan tattalin arziki a matsayin babban dalilin da ya haddasa rashin kwanciyar hankali a wasu wuraren kasar.

  • Japan Ba Ta Boye Yunkurinta Na Yin Fito-na-fito Da Kasar Sin Ba

Abin lura shi ne, ba Najeriya ce kadai ke fuskantar matsalar tattalin arziki ba. A halin yanzu, annobar COVID-19 da yakin da ake yi tsakanin Rasha da Ukraine, sun jefa tattalin arzikin duniya cikin wani yanayi na rashin tabbas. Idan muka dubi alkaluman da aka samu a kwanakin nan, za mu ga jimillar GDP ta kasar Amurka ta ragu da kaso 1.4, sa’an nan yadda bankin tsakiya na kasar ya dauki matakai don daidaita matsalar hauhawar farashin kayayyaki, ya sa kasuwar hannayen jari ta kasar ta gamu da babbar matsala, inda farashin kusan dukkan hannayen jari ya ragu sosai. Yayin da a kasar Birtaniya, hauhawar farashin kayayyaki ta sa bankin Ingila ya daga jimillar ruwan da ake bayar kan kudin ajiya zuwa wani matsayin da ba a taba ganin irinsa ba cikin wasu shekaru 13 da suka wuce, tare da sanar da tabarbarewar tattalin arzikin kasar. A cikin wannan yanayi mai wuya da ya shafi dukkan kasashe, ya kamata a yi kokarin yin hangen nesa, da daukar nagartattun matakai, da hadin gwiwa da sauran kasashe yadda ake bukata.

Dole ne a magance matakai na son kai, da ma rashin hangen nesa. Misali, a Najeriya, wasu matasa sun dauki makamai sun zama ‘yan fashi sakamakon kwadayi. Amma idan ana da hangen nesa, za a iya ganin cewa ayyukan da suke yi sun haifar da barna ga jama’a, kana nan gaba tabbas za a yanke musu hukunci bisa muggun ayyukan da suka aikata. Ban da wannan kuma, misali a kasar Amurka, gwamnati ta bari cutar COVID-19 ta haddasa asarar rayukan mutane fiye da miliyan 1, da raunana tattalin arziki, tana neman raya tattalin arzikin kasar ta hanyar zuba makudan kudi cikin kasawanni kawai amma ba tare da daukar matakai na hana bazuwar annoba ba, abun da ya sa ake fama da matsalar hauhawar farashin kayayyaki mai tsanani a kasar. Sa’an nan, wasu kasashen yammacin duniya, yayin da suke fuskantar koma bayan tattalin arziki, suna neman ta da rikici tsakanin sauran kasashe, da raunana tattalin arzikinsu, don neman sanya karin jari komawa cikin kasuwannin gida. Amma a hakika, bayan an samu barkewar yaki a wani yanki, lamarin ya kan kawo cikas ga aikin samar da kayayyaki na duniya, da haifar da illa ga tattalin arzikin kasashe daban daban.

Dalilin da ya sa kasar Sin ke iya samun ci gaban tattalin arzikinta cikin matukar sauri, cikin shekaru fiye da 40 da suka wuce, shi ne domin hangen nesa da ta yi, abin da ya sa take iya daukar nagartattun matakai masu dorewa, da daidaita moriyarta da ta sauran kasashe. Yayin da take hulda da kasashen Afirka, kasar Sin ta tsayawa kan manufar “tabbatar da daidaito, da moriyar dukkan bangarori”. Tana fatan ganin kasashen Afirka sun samu ci gaban tattalin arizki, kana tana goyon bayan hadin gwiwar da kasashen Afirka suke yi da sauran kasashe. Idan mun dauki bashin da kasar Sin ta ba kasashen Afirka a matsayin misali, za mu ga cewa, ko da yake kafofin watsa labaru na kasashen yamma su kan bayyana shi a matsayin “mulkin mallaka” da “tarkon bashi”, a hakika kasar Sin na ba da bashi ne bisa ainihin bukatun da kasashen Afirka suke da shi, da taimakawa kasashen Afirka inganta kayayyakin more rayuwa: Tun daga shekarar 2000, kamfanonin kasar Sin sun taimaki kasashen Afirka wajen gina ko kuma inganta layin dogo na fiye da kilomita dubu 10, da hanyoyin mota kimanin kilomita dubu 100, da gadaje kimanin dubu 1, da tashoshin jiragen ruwa 100, dai dai sauransu. Sa’an nan idan wata kasa ta gamu da matsalar biyan bashi, kasar Sin za ta tattauna da ita don samar da wata dabara mai dacewa don daidaita batun, har ma ta kan yafe wa kasa maras karfi bashin da take binta.

Hangen nesa ne ya sa kasar Sin take son zuba jari don tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashen Afirka, gami da ba da damar samun ci gaban harkoki ga kamfanonin kasar. (Bello Wang)

Labarai Masu Nasaba

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Amurka Kan Sin Ya Shaida Yunkurinta Na Tada Rikici Da Manufar Kama Karya

Next Post

Sin Ta Karyata Ikirari Da Canada Ta Yi Na Cewa Wai Wani Jirgin Sojin Sin Ya Tare Jirgin Sojinta

Related

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

21 hours ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

22 hours ago
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

23 hours ago
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

2 days ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

2 days ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

2 days ago
Next Post
Sin Ta Karyata Ikirari Da Canada Ta Yi Na Cewa Wai Wani Jirgin Sojin Sin Ya Tare Jirgin Sojinta

Sin Ta Karyata Ikirari Da Canada Ta Yi Na Cewa Wai Wani Jirgin Sojin Sin Ya Tare Jirgin Sojinta

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.