Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin, ya ce tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya kawo hadin kai a jam’iyyar APC.
Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa ne a ranar 3 ga watan Agusta, 2023, yayin taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar (NWC) da aka gudanar a Abuja.
- Kirsimeti: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Shinkafa Don Tallafa Wa Kiristoci
- ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna
Sanata Barau a wani sako da ya aikewa Ganduje a ranar bikin cikarsa shekaru 75 da haihuwa ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Ismail Mudashir, ya ce, Ganduje ya jagoranci jam’iyyar zuwa nasara a zaben gwamnonin jihohin Edo, Ondo, Kogi da kuma Imo.
Don haka, Sanata Barau ya nemi Ganduje da ya kara azama wajen lashe sauran jihohin da suka yi wa jam’iyyar tutsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp