• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan ‘Labarin LEADERSHIP’ Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

bySadiq
1 year ago
inManyan Labarai
0
Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan ‘Labarin LEADERSHIP’ Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

Muhammadu Sanusi II, ya bari garin Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas a gaggauce, jim kadan bayan ya gabatar da jawabinsa a babban taron tattalin arziki da zuba jari a jihar.

Sanusi yana tsakiyar gabatar da jawabinsa ne, ‘labarin LEADERSHIP’ na sake nada shi a matsayin Sarkin Kano, ya karade gari.

  • Da Ɗumi-Ɗumi: An Sake Naɗa Sanusi Lamido Sanusi A Matsayin Sarkin Kano
  • Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

LEADERSHIP, ta bayyana cewar, an tsaurara tsaro a tattare da Sanusi lokacin da yake barin wajen taron da ke gudana a Obi Wali International Conference Center a Fatakwal, wanda hakan ya sa ‘yan jarida ba su samu damar tattaunawa da shi ba.

A halin da ake ciki, Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya taya Sanusi II murnar sake zama Sarkin Kano.

Fubara, a wata sanarwa da ya fitar a Fatakwal, ya ce ya samu labarin sake nada tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), a matsayin Sarkin Kano, wanda hakan ya sanya shi farin ciki matuka.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

Gwamnan, ya kara da cewa sake nada shi sarautar da gwamnatin jihar ta yi, ya nuna cewa tsige Muhammadu Sanusi II da aka yi a ranar 9 ga watan Maris, 2020, bai yi wa al’ummar Jihar Kano dadi ba, wanda ya ce rashin adalci ne ga miliyoyin al’ummar jihar.

Ya yaba wa gwamnatin Jihar Kano bisa yadda ta saurari bukatun jama’a, tare da yin gyara kan abin da aka yi a baya, sannan ya bukaci jama’a da su bai wa Sarkin goyon baya domin samun nasara.

Fubara, ya kuma bukaci shugaban darikar Tijjanniya na Nijeriya, Muhammad Sanusi II da ya jagoranci mabiya darikar sama da miliyan 50 a Nijeriya cikin hikima da jajircewa tare da samar da zaman lafiya da adalci a tsakanin kowa a Kano.

Ya kuma yi wa Sarkin Kano na 14 fatan samun nasara tare da samar da ci gaba ga al’ummar jihar.

Tags: kanoMasarautaMulkiRibasSanusi II
ShareTweetSendShare
Sadiq

Sadiq

Related

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

7 hours ago
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 
Manyan Labarai

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

19 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Rizhao Dake Lardin Shandong

Xi Jinping Ya Yi Rangadi a Birnin Rizhao Dake Lardin Shandong

LABARAI MASU NASABA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.