Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya naɗa Alhaji Mannir Sanusi a matsayin sabon Galadiman Kano, ɗaya daga cikin manyan sarautun gargajiya a masarautar Kano.
Naɗin ya biyo bayan rasuwar Galadiman Kano na baya, Abbas Sanusi.
- Li Qiang Ya Tattauna Da Shugabar Kwamitin EU
- ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Satar Mota A Bauchi
Kafin wannan lokaci, Mannir Sanusi shi ne Hakimin Bichi, kuma ana yabonsa da shugabanci nagari.
Sauran sabbin naɗe-naɗen sun haɗa da:
- Turakin Kano ya zama Wamban Kano
- Adam Sanusi ya zama Tafidan Kano
- Ahmad Abbas ya zama Yariman Kano
Sarkin ya taya sabbin masu sarautun murna tare da jan hankalinsu da su yi aiki da gaskiya da kishin al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp