Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Saad Abubakar lll, ya umarci al’ummar musulmi da su fara neman jinjirin watan Safar na shekarar Musulunci ta 1444 daga yau Asabar 27/08/2022 daidai da kalandar Musulunci 29 Muharram 1444AH.
Sarkin ya bayyana haka a wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin Addini na Sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Wali Junaidu.
Sanarwar ta ce idan an samu bayanan ganin wata sai a mika wa hakimin ko shugaban gunduma mafi kusa domin tuntubar Mai alfarma Sarkin Musulmi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp