ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hikimar Rabe Farkon Shekarar Musulunci Da Ranar Fara Aiken Manzancinsa (SAW)

by Sulaiman and Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
4 years ago
Musulunci

Masu karatu har yanzu dai muna kan bayani game da abubuwan da suka sa Sahabbai ba su kafa tarihin kirgen shekarar musulunci ba da wasu manyan alherai na Musulunci, sai suka zabi Muharram ta zama farkon shekarar tare da lakaba mata shekarar Hijirah.

A makon da ya gabata mun yi bayani kan hikimar ware farkon shekarar daga watan Rabi’ul Auwal zuwa watan Muharram saboda girman haihuwar Manzon Allah (SAW). A yau kuma, za mu ci gaba da bayani a kan ware kirgen farkon shekarar daban da ranar da aka fara aiken Manzanci ga Annabi (SAW).

  • Mai Gadin Kabarin Manzon Allah SAW Ya Rasu

Tun ana sauran shekara uku Manzon Allah (SAW) ya cika shekara 40 da haihuwa, ya rika fita zuwa Halwa (kadaita) a wajen garin Makka a cikin Kogon Hira, mai nisan mil shida daga cikin garin na Makka.

ADVERTISEMENT

Manzon Allah a lokacin ya bar gida, ya bar iyali, ya bar kowa domin ya kadaita da Ubangijinsa.
Wannan Kogon Hirar, lokacin da muka yi Hajji a 2004, mun ziyarci Kogon, muna yin Sallar Asuba muka fito amma ba mu kai ba sai wurin karfe takwas. Ga motoci na wucewa da komai amma kuma saboda dajin wurin ga birori ne suna ta tsalle-tsalle.

To, mai karatu ka yi tunani da kwakwalwarka, a 2004 ga wasu namun daji nan har yanzu a wurin, to ina ga in an koma sama da shekara dubu daya da dari biyar, yaya wajen nan ya kasance kenan? Amma haka Annabi (SAW) zai je wajen kuma idan ya tafi ba a kasan dutsen yake zama ba sai ya hau samansa, an bar gari, an bar iyali, an bar dangi, yanzu ma an bar kan kasa ma bakidaya.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Shi ma dutsen ba a zauna a sararinsa ba sai da aka shiga kogonsa, Subhanallah! In ka je hanyar shiga Kogon ma za ka ji kana hawaye saboda tafakurrin wadannan abubuwan na Manzon Allah (SAW).

Haka Annabi (SAW) yake zama a cikin Kogon, ya yi wata daya zuwa wata uku har sai abincinsa ya kare. Akwai ruwayar Sayyidina Aliyu (Karramallahu wajhahu) da ya ce idan abincin Manzon Allah ya kare shi yake kai masa.

Kuma ya ce tun a wannan lokacin yakan ji wani irin kamshi a wurin wanda babu irinsa a Makka. Haka Manzon Allah ya ci gaba da yi har Hakku ya yi masa tajalli fatahi ya samu.

Malaman Tafsiri kuma suka ce har Mala’ika Jibrilu ya zo masa. Ya ce masa “yi karatu”, Manzon Allah ya ce masa “ni ba mai karatu ba ne”, sai da aka yi haka sau uku kafin ayoyin nan na Suratu Ikra’a suka sauka masa (SAW). Daga nan fa sai Duniya ta yi wani irin numfashi, Manzon Allah (SAW) ya fara karantar da mu al’ummarsa da Larabci abubuwan da ya samu daga Ubanginjinsa tare da nuna mana kyawawan dabi’u.

A wannan lokacin da yake zuwa Halwa a Kogon Hira ibada ce ta Tafakkuri yake yi (Malamai sun ce da akwai wani abu da zai fi La’ilaha illallahu, zai zama Tafakkuri ne). Don haka babu wanda zai ce babu Halwa a Musulunci.

Idan dai mutum zai nemi sanin hukunce-hukuncen ibada ne, ya tafi wurin Malamai, ba zai samu wannan a Halwa ba. Amma idan zai nemi sanin wani abu mai zurfi ne na Imani to wannan sai da kebancewa (Halwa).

Yanzu mutum ya yi tunani, kafin Manzon Allah (SAW) ya kawo mana addinin nan, sai da ya bar iyali, ya bar gari, ya bar kowa ya tafi kogon dutse ya yi Halwa ta shekara uku, to wani ya zo da rana tsaka ya yi shigar burtu ya ce mana ya san komai na addinin, abin da ya ga dama shi ne mai kyau, wanda bai ga dama ba haramun ne, yaushe hankali zai kama wannan ballantana imani? Ba don Rahamar Manzon Allah da ya ce ya bar mu a hanya mai sauki ba, yaushe addinin zai samu mana. Kuma dai duk da saukin addinin yana da hawa-hawa, Islam, Iman da Ihsan.

Don haka ba komai na addini za ka ce ka sani ba, dole akwai iya gejinka na Islam, haka nan a Iman sannan ga kuma Ihsan ba adadi. Wani ma ya ce ba ilimin badini a cikin addini, yanzu Manzon Allah ya zauna ne a gida a gaban mata da yara addinin ya sauka? Ai sai da ya bar gida ya shiga Kogon Dutse ya yi Halwa. Kuma ba Manzon Allah shi kadai ba, sauran Annabawa ma haka ne.

Har gara Kogon Hira ma a kusa yake idan aka kwatanta da Dutsen Duri Sina’a, wurin da Annabi Musa (AS) ya yi magana da Allah. Cikin dajin da mutum mai tsoro ba zai iya zuwa ba, ko a yanzu dubi yadda wurin yake balle a wancan lokacin nasu.

Dubi Annabi Ibrahim, daga Isra’ila ya dauko mace da danta zai musu gida kawai amma sai da ya shafe wurin mil dubu hudu ya kawosu Makka ya ajiye. Don haka abubuwa na Annabawa da bin hanyarsu ba a sa dan karamin hankalinka a ciki.

Daga wannan Halwar ce Manzon Allah (SAW) ya zo mana da duk alheran da duniya ta sauyu da su. Larabawan da ba su iya karatu da rubutu ba suka zama Malamai.

Daulolin da suka zama suna mulkar Larabawan duk suka juya suka zama a karkashinsu, sun samu yalwa na abinci maimakon gurasa da busasshen nama kawai da suke ci a da. Ko a baya-bayan nan ma, shugaban Hadaddiyar Daular Laraba (marigayi) Bin Zayed, ya roki Shehu Ibrahim Inyass (RA) ya yi musu addu’a saboda kasarsu ba ta da komai na arziki, Shehu ya ba shi Darikar Tijjaniyya ya yi masa addu’a ya ce komai zai zo muku. Su manyan kasar sun san haka kuma wasu har yau suna rike da alkawari.

A shekarar da aka aiko Manzon Allah (SAW), shekarar giwa tana da 40, shekarar haihuwar Annabi Isah kuma tana da 611. Allah ya ba Manzon Allah Alkur’ani wanda sai dai mu dan tsakuri abin da za mu iya a cikinsa, mu dauki zahirinsa da ya yi mana magana a kan hukunce-hukuncen ibadu da sauran mu’amaloli, sai dai mu yi wanka a bakin koginsa kawai, amma fa a Kogon Hira aka debo shi, shekara uku ana Halwa dominsa duk da karfin annabta.

Allah ya ce, wannan Alkur’anin “Littafi ne da aka saukar a gare ka (SAW) don ka fitar da mutane daga cikin duffai (mai yawa), ka shigar da su haske (guda daya) da izinin Ubangijinka (abin ba zai yiwu ba in ba izinin Ubangiji) izuwa tafarkin Mabuwayi abin godiya. Shi ne Allah mai mallakar komai da komai da ke cikin sammai da kasa”.

Wannan aya sirrin aiken Manzon Allah (SAW) yana cikinta.
Wannan Alkur’ani shi ne tsarin mulkin da ya shafe kowane irin tsarin mulki duka, shi ne ya tsere wa dukkan sauran littafan da suka zo daga Allah.

Ya shafe duk wani tunani na masu falsafa irinsu Aristotle, Karl Mad, da su Bictor Couzen da Khalidr Ruhi, Nepolion, William John, duk Alkur’ani ya shafe su.

Haka nan duk wanda ba a cikin Alkur’anin ne zai yi tafakkuri ya fito da abubuwa ba, Alkur’ani ya shafe shi daga nan har tashin kiyama. Don haka mu so Allah, mai rahama ne, mai jinkai ne komai nasa mai sauki ne. Sannan duk mai son komai nasa ya yi dai-dai, ya debo a cikin Alkur’ani.

To duk da wadannan alherai na sirrin aike, Sahabbai sun ajiye kirgen shekarar musulunci ne da Hijirah saboda hikima.

Musulunci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Musulunci
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ posts Bio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Musulunci
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Kisan Gilla: Abin Da Sheikh Aisami Ya Tambaye Ni Kafin In Ja Kunamar Bindiga Na Harbe Shi

DA DUMI-DUMI: Rundunar Sojin Nijeriya Ta Kori Sojojin Da Ake Zargi Da Kashe Sheikh Aisami

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.