ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Noman Gaya Ya Nemi Gwamna Abba Ya Bullo Da Sabon Tsarin Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
2 years ago
Sarkin noman gaya

Shawarar mu ga gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Abba Gida-Gida ita ce a yi wa manoman Kano sabon tsarin bunkasa noma a zamanin mulkinsa wanda manoman ba za su taba mantawa da shi ba kamar aikin marigayi Alhaji Audu Bako.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Sarkin Noman Masarautar Gaya, Alhaji Ibrahim Yakubu Tagahu a zantawarsa da wakilinmu.
Ya ci gaba da cewa, “domin Kano dai na da ginshikai, kamar Ilimi, Karatu, Noma, Sarauta, Kasuwanci, kuma akasarin mutanan Kano manoma ne da `yan kasuwa kuma yanzu haka an kiyasta Kano tana da albarkar yawan jama`a da suka kai kimanin Miliyan 20 a kiyasi, duk da rabon Kano da kidayar jama`a tun shekarar 2006 yau kimani shekara 17 kenan wanda ina ganin cewa a kiyasin muna da manoma a Kano za su haura miliyan 15 wanda ka ga sunfi yawan mutanan wasu kasashe da dama a duniya a mahangar mu ta manoma da mu ke zama a yankunan karkara.

  • Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

Bayan ya yi murnar kammala zaban shugaban kasa da na `yan majalisar dattawa da na wakilai na tarayya da na jihohi da kuma gwamnoni lafiya a Nijeriya, Alhaji Ibrahim ya ce abin da yake kara faranta musu rai game da zaben shi ne, “a ciki ne aka zabi mai girma gwamnan Jahar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Abba Gida- Gida wanda kuma danmu ne kuma jikanmu ne idan aka yi la`akari da tarihin sabon gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusif mai alaka ko tarihi da masarautar Gaya da ta Kano baki daya.”

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “Babu shakka kowa ya san Kano kasa ce mai albarkar noma da fadin kasa mai karbar shuka kowa ne iri na duniya a kyakkyawan zato na idan aka shuka shi a Kano za yi bisa la`akari da shuke-shuken da mu ke na rani da na damina tun daga kan Dawa, Gero, Masara, Shinkafa, Dauro, Maiwa, Wake, Gyada, Waken suya, Accha,Alkama a noman rani, da sauran nau`o`i iri-iri na kayan abinci mai kwaya.

“Haka kuma a Kano ana noman gyada wanda Kano na noma gyada a kalla 60 cikin 100 na noman gyada a Nijeriya muna noman auduga duk a noman damuna a Kano a na noman Rogo, Makani, Gwaza, haka a na noman dankali a Kano, ana noma Albasa, yakuwa, Doborodo, Rama, Zogale, da sauransu haka a Kano ne ake noman rake noman takanda, haka a laiyahu da dai sauransu wanda wadannan abubuwa idan aka samu tsari na gwamnatin Kano ko ta tarayya a gona daya za a iya samar wa miliyoyin matasa aikin yi wanda za a dogara da kai ba tare da ragaita zuwa ofis ko kamfanoni neman aiki ba. Wannan kuma ba zai yiwu ba sai da kyakkawan tsari na gwamnatin Kano ta Abba Gida-Gida koma ta gwamnatin tarayya karkashin Shugaban Kasa Ahmad Bola Tunubu.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Da ya juya kan matsalolin manoman Kano kuwa, Sarkin Noman na Gaya ya ce, “Kadan daga cikin Matsalolin manoman Kano da mu ke son a kawo mana kyakkyawan tsari na tallafa mana akwai karancin motocin noma da kayan aiki na zamani karancin guraran noman rani bisa la`akari da yadda Kano ta ke da dam-dam wato madatsun ruwa wanda aka gina su tun zamanin marigayi Audu Bako tun lokacin da Kano ta zama jiha a shekarar 1966 suke wanda suna da bukatar a yashe su a tsattsaga su domin fadada gurin noma ga dimbin matasanmu na Kano.

“Haka tsarin tallafa wa manoma duk lokacin da gwamnatin Abba Gida-Gida za ta yi ko ta Tunubu, wajibi ne a samo a halin abun kamar manoma, da shugabannin su da sarakunan su, da kuma sarakuna iyayen al`umma da sauran shugaban ni wanda al`umma ke ganin kimarsu amma sanya siyasa wajan raba tallafin noma mu dai manoma na gaskiya ba ma amfana da wannan tsari kuma yau manoma na fama da tsadar taki, tsadar irin, tsadar maganin ciyawa, da sauran kayayyaki da manoma su ke amfani da su yau sun yi tsada wanda a neman kyakkyawan tsari na tallafa wa manoman Kano dan bunkasawa.

“Haka zalika shawarar mu duk wanda za a bawa kwamishina na ma`aikatar gona da sauran shugabanci na KASCO Da KANARDA da sauran cibiyoyin bunkasa noma a Kano a bawa wanda ya san harkar, mai kishin harkar, hakan zai taimaka wa mu manoma haka kuma mu na yaba wa sabon gwamnan Kano kan kishinsa na ilimi, lafiya, tattalin arziki, kasuwanci, ruwan sha, Taswiyyarar Kano, Tsaro, Samar da aikin yi ga matasa da dai sauransu kan yadda muka ga ya himmatu da hawansa gwamnan Kano.” In ji shi.

A karshe, sarkin noman masarautar noman Gaya Alhaji Ibrahim Yakubu Tagahu, ya ce “a madadan sarkin Gaya Dr. Ibrahim Abdulkadir muna yi wa Alhazan bana da suka sauke farali da mu wadanda muka yi Sallar Layya, muna yi wa masarautar Gaya, masarautar Kano, da Jihar Kano da Nijeriya fatan samun wadataccan tsaro da zaman lafiyar al`ummar Nijeriya baki daya.” Ya bayyana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 

Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma'aikatan Kano 

LABARAI MASU NASABA

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.