ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Noman Gaya Ya Nemi Gwamna Abba Ya Bullo Da Sabon Tsarin Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
3 years ago
Sarkin noman gaya

Shawarar mu ga gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Abba Gida-Gida ita ce a yi wa manoman Kano sabon tsarin bunkasa noma a zamanin mulkinsa wanda manoman ba za su taba mantawa da shi ba kamar aikin marigayi Alhaji Audu Bako.

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Sarkin Noman Masarautar Gaya, Alhaji Ibrahim Yakubu Tagahu a zantawarsa da wakilinmu.
Ya ci gaba da cewa, “domin Kano dai na da ginshikai, kamar Ilimi, Karatu, Noma, Sarauta, Kasuwanci, kuma akasarin mutanan Kano manoma ne da `yan kasuwa kuma yanzu haka an kiyasta Kano tana da albarkar yawan jama`a da suka kai kimanin Miliyan 20 a kiyasi, duk da rabon Kano da kidayar jama`a tun shekarar 2006 yau kimani shekara 17 kenan wanda ina ganin cewa a kiyasin muna da manoma a Kano za su haura miliyan 15 wanda ka ga sunfi yawan mutanan wasu kasashe da dama a duniya a mahangar mu ta manoma da mu ke zama a yankunan karkara.

  • Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

Bayan ya yi murnar kammala zaban shugaban kasa da na `yan majalisar dattawa da na wakilai na tarayya da na jihohi da kuma gwamnoni lafiya a Nijeriya, Alhaji Ibrahim ya ce abin da yake kara faranta musu rai game da zaben shi ne, “a ciki ne aka zabi mai girma gwamnan Jahar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Abba Gida- Gida wanda kuma danmu ne kuma jikanmu ne idan aka yi la`akari da tarihin sabon gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusif mai alaka ko tarihi da masarautar Gaya da ta Kano baki daya.”

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “Babu shakka kowa ya san Kano kasa ce mai albarkar noma da fadin kasa mai karbar shuka kowa ne iri na duniya a kyakkyawan zato na idan aka shuka shi a Kano za yi bisa la`akari da shuke-shuken da mu ke na rani da na damina tun daga kan Dawa, Gero, Masara, Shinkafa, Dauro, Maiwa, Wake, Gyada, Waken suya, Accha,Alkama a noman rani, da sauran nau`o`i iri-iri na kayan abinci mai kwaya.

“Haka kuma a Kano ana noman gyada wanda Kano na noma gyada a kalla 60 cikin 100 na noman gyada a Nijeriya muna noman auduga duk a noman damuna a Kano a na noman Rogo, Makani, Gwaza, haka a na noman dankali a Kano, ana noma Albasa, yakuwa, Doborodo, Rama, Zogale, da sauransu haka a Kano ne ake noman rake noman takanda, haka a laiyahu da dai sauransu wanda wadannan abubuwa idan aka samu tsari na gwamnatin Kano ko ta tarayya a gona daya za a iya samar wa miliyoyin matasa aikin yi wanda za a dogara da kai ba tare da ragaita zuwa ofis ko kamfanoni neman aiki ba. Wannan kuma ba zai yiwu ba sai da kyakkawan tsari na gwamnatin Kano ta Abba Gida-Gida koma ta gwamnatin tarayya karkashin Shugaban Kasa Ahmad Bola Tunubu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Da ya juya kan matsalolin manoman Kano kuwa, Sarkin Noman na Gaya ya ce, “Kadan daga cikin Matsalolin manoman Kano da mu ke son a kawo mana kyakkyawan tsari na tallafa mana akwai karancin motocin noma da kayan aiki na zamani karancin guraran noman rani bisa la`akari da yadda Kano ta ke da dam-dam wato madatsun ruwa wanda aka gina su tun zamanin marigayi Audu Bako tun lokacin da Kano ta zama jiha a shekarar 1966 suke wanda suna da bukatar a yashe su a tsattsaga su domin fadada gurin noma ga dimbin matasanmu na Kano.

“Haka tsarin tallafa wa manoma duk lokacin da gwamnatin Abba Gida-Gida za ta yi ko ta Tunubu, wajibi ne a samo a halin abun kamar manoma, da shugabannin su da sarakunan su, da kuma sarakuna iyayen al`umma da sauran shugaban ni wanda al`umma ke ganin kimarsu amma sanya siyasa wajan raba tallafin noma mu dai manoma na gaskiya ba ma amfana da wannan tsari kuma yau manoma na fama da tsadar taki, tsadar irin, tsadar maganin ciyawa, da sauran kayayyaki da manoma su ke amfani da su yau sun yi tsada wanda a neman kyakkyawan tsari na tallafa wa manoman Kano dan bunkasawa.

“Haka zalika shawarar mu duk wanda za a bawa kwamishina na ma`aikatar gona da sauran shugabanci na KASCO Da KANARDA da sauran cibiyoyin bunkasa noma a Kano a bawa wanda ya san harkar, mai kishin harkar, hakan zai taimaka wa mu manoma haka kuma mu na yaba wa sabon gwamnan Kano kan kishinsa na ilimi, lafiya, tattalin arziki, kasuwanci, ruwan sha, Taswiyyarar Kano, Tsaro, Samar da aikin yi ga matasa da dai sauransu kan yadda muka ga ya himmatu da hawansa gwamnan Kano.” In ji shi.

A karshe, sarkin noman masarautar noman Gaya Alhaji Ibrahim Yakubu Tagahu, ya ce “a madadan sarkin Gaya Dr. Ibrahim Abdulkadir muna yi wa Alhazan bana da suka sauke farali da mu wadanda muka yi Sallar Layya, muna yi wa masarautar Gaya, masarautar Kano, da Jihar Kano da Nijeriya fatan samun wadataccan tsaro da zaman lafiyar al`ummar Nijeriya baki daya.” Ya bayyana.

Sarkin noman gaya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma’aikatan Kano 

Gwamnatin Kano Za Ta Bincike Dakatar Da Albashin Ma'aikatan Kano 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.