• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saurayi Ya Babbake Gawar Budurwarsa Bayan Dirka Mata Ciki A Bauchi

Ya Kashe Ta Sannan Ya Babbake Gawarta

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai, Al'ajabi
0
Dalibi Ya Daba Wa Wasu Dalibai 2 Wuka A Kan Musun Kwallon Kafa A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar cafke wani saurayi mai shekara 27 a duniya, Munkaila Ado bisa zargin kashe budurwarsa mai suna Safiya Danladi, ‘yar shekara 13 a duniya da ke kauyen Pali a karamar hukumar Alkaleri a cikin garin Bauchi. 

Bayanai sun nuna cewa kafin safiya ta mutu tana dauke da cikin watanni hudu wanda kuma shi saurayin nata ne ya mata.

  •  Sharhi: Siyasar Ubangida Da Zaben Shekarar 2023
  • Za A Dawo Da Shingen Binciken ‘Yansanda A Fadin Nijeriya

A sanarwar da kakakin ‘yansadan Bauchi, Ahmed Wakil ya fitar, ya ce Munkaila ya dauki Safiya zuwa jihar Gombe domin zubar da cikin da ya mata, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba.

Daga baya kuma, Munkaila Ado ya yanke hukuncin kashe ta bayan rashin nasarar zubar da cikin da ya yi wa budurwar tasa.

Sanarwar ta ce, “Wanda ake zargi (Munkaila) ya bayyana da kansa cewa yarinyar da ta bace din budurwarsa ce da take dauke da cikin watanni hudu da sanin mahaifiyarta ya yi kokarin zubar da cikin, shi kuma mahaifinta Alhaji Danladi Mohammed ba shi da masaniya.”

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Sanarwar ta ci gaba da cewa “Munkaila ya hada baki da mahaifiyar yarinyar ‘yar shekara 13 da wani mai suna Muazu, inda suka dauki yarinyar zuwa Gombe da nufin zubar da cikin.

“Bayan da suka isa Gombe sun samu wata mata mai suna Hajiya Amina Abubakar mai shekara 50 da gidanta ke Jekada Fari da ke bayan asibitin Kwararru na Gombe, inda aka yi wa yarinyar wasu abubuwa da nufin zubar da cikin”.

Bayan rashin nasarar zubar da cikin, sanarwar ta kara da cewa a lokacin da suke hanyar dawowa Bauchi, Munkaila da Muazu suka shake Safiya har ta mutu.

Daga baya kuma suka kona gawarta sannan suka binne ta a wani rami.

‘Yansandan sun kara da cewa za su gurfanar da wadanda suka kama a gaban kotu bisa tuhumarsu da kisan kai gami da cin zarafi da keta haddin karamar yarinya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaBabbakaBauchiBudurwaGawaGombeKisaMahaifiyaMatashiZubar Da Ciki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jayati Ghosh: Manufofin Kudi Na Amurka Suna Haddasa Hadari Ga Sauran Kasashe

Next Post

Kyamar ‘Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature

Related

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

2 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

20 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

2 days ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

3 days ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

3 days ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

3 days ago
Next Post
Kyamar ‘Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature

Kyamar 'Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature

LABARAI MASU NASABA

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.