ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saurayi Ya Babbake Gawar Budurwarsa Bayan Dirka Mata Ciki A Bauchi

Ya Kashe Ta Sannan Ya Babbake Gawarta

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Saurayi

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar cafke wani saurayi mai shekara 27 a duniya, Munkaila Ado bisa zargin kashe budurwarsa mai suna Safiya Danladi, ‘yar shekara 13 a duniya da ke kauyen Pali a karamar hukumar Alkaleri a cikin garin Bauchi. 

Bayanai sun nuna cewa kafin safiya ta mutu tana dauke da cikin watanni hudu wanda kuma shi saurayin nata ne ya mata.

  •  Sharhi: Siyasar Ubangida Da Zaben Shekarar 2023
  • Za A Dawo Da Shingen Binciken ‘Yansanda A Fadin Nijeriya

A sanarwar da kakakin ‘yansadan Bauchi, Ahmed Wakil ya fitar, ya ce Munkaila ya dauki Safiya zuwa jihar Gombe domin zubar da cikin da ya mata, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba.

ADVERTISEMENT

Daga baya kuma, Munkaila Ado ya yanke hukuncin kashe ta bayan rashin nasarar zubar da cikin da ya yi wa budurwar tasa.

Sanarwar ta ce, “Wanda ake zargi (Munkaila) ya bayyana da kansa cewa yarinyar da ta bace din budurwarsa ce da take dauke da cikin watanni hudu da sanin mahaifiyarta ya yi kokarin zubar da cikin, shi kuma mahaifinta Alhaji Danladi Mohammed ba shi da masaniya.”

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Sanarwar ta ci gaba da cewa “Munkaila ya hada baki da mahaifiyar yarinyar ‘yar shekara 13 da wani mai suna Muazu, inda suka dauki yarinyar zuwa Gombe da nufin zubar da cikin.

“Bayan da suka isa Gombe sun samu wata mata mai suna Hajiya Amina Abubakar mai shekara 50 da gidanta ke Jekada Fari da ke bayan asibitin Kwararru na Gombe, inda aka yi wa yarinyar wasu abubuwa da nufin zubar da cikin”.

Bayan rashin nasarar zubar da cikin, sanarwar ta kara da cewa a lokacin da suke hanyar dawowa Bauchi, Munkaila da Muazu suka shake Safiya har ta mutu.

Daga baya kuma suka kona gawarta sannan suka binne ta a wani rami.

‘Yansandan sun kara da cewa za su gurfanar da wadanda suka kama a gaban kotu bisa tuhumarsu da kisan kai gami da cin zarafi da keta haddin karamar yarinya.

Saurayi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya
Manyan Labarai

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Next Post
Kyamar ‘Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature

Kyamar 'Yan Shaye-shaye Ke Kara Tsunduma Matasa Ayyukan Assha -Fatima Bature

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.