• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saurayi Ya Kashe Budurwarsa A Kan 5000 A Bauchi

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani matashi mai shekaru 19 mai suna Mohammed Ibrahim, mazaunin Sabon-Layi da ke wajen birnin Bauchi a Jihar Bauchi, ya daba wa budurwarsa mai suna Emmanuella Ande wuka har lahira bayan wani rikici da ya barke a tsakaninsu kan kudi naira 5,000.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kafin faruwar lamarin, Mohammed ya sace kusan Naira 400,000 na mahaifinsa domin ya kashe wa Emannuella, wadda ‘yar Jihar Filato ce, bayan sun shirya haduwa a Fatakwal a Jihar Ribas.

  • Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba
  • Gwamnati Ta Shirya Fatattakar ‘Yan Bindiga A Duk Inda Suke – Ministan Tsaro

Mohammed wanda yanzu haka yana hannun ‘yansanda, ya hadu da marigayiyar ne a shafukan sada zumunta kafin daga bisani suka hadu a wani wurin shakatawa da ke unguwar Bayan-Gari a Bauchi.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Laraba, ya ce wanda ake tuhumar ya kuma daba wa wani Zaharadeen Adamu mai shekaru 36 wuka, wanda ya yi kokarin ceton Emmanuella.

“Wannan mummunan al’amari ya faru ne a lokacin da wadda aka kashe ta bukaci kudi naira 5000 yayin da ita budurwar ta nemi ya biya ta wasu da ta ke bin sa, hakan ne ya sa cacar-baki ta kaure har fads ya shiga tsakaninsu lamarin da ya yi sanadin da ya sa ta samu rauni wanda ya kai ga mutuwarta.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

“Ya daba wa budurwarsa Emmanuella Ande ‘yar Jihar Filato, wuka a kusa da kirjinta, a lokacin ne budurwar ta yi kururuwa, mutanen da ke wajen suka yi yunkurin kai mata dauki, suka bude kofar da karfi, inda wanda ake zargin ya kuma daba wa daya daga cikinsu wuka.

“Tawagar ‘yansanda ta yi gaggawar kai dauki, inda suka dauki budurwar zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) Bauchi, inda aka tabbatar da mutuwarta.

“Haka zalika, an kwantar da Zaharadeen kuma an yi masa magani a asibitin an kuma sallame shi, a halin yanzu ana bincike a kan lamarin,” in ji kakakin.

SP Wakil ya ce an samu wuka daga hannun Mohammed, inda ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar kammala bincike, za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiBudurwaFilatoKisaMatashiSaurayiWuka
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Taron Koli Game Da Ayyukan Raya Karkara A Sin

Next Post

Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

3 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

5 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

5 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

6 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

9 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

11 hours ago
Next Post
Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.