• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauya Fasalin Dimokuradiyyar Afirka: Lokaci Ya Yi Da Za Mu Yada Kwallon Mangwaro Mu Huta Da Kuda

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Manyan Labarai, Ra'ayi Riga
0
Sauya Fasalin Dimokuradiyyar Afirka: Lokaci Ya Yi Da Za Mu Yada Kwallon Mangwaro Mu Huta Da Kuda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun daga watan Nuwamban 2023 har zuwa Mayun 2024, duk wanda yake bibiyar manyan tarurruka da suka jibanci fafutukar neman mafita a kan matsalolin da suka addabi al’umma musamman ta fuskar shugabanci a Nijeriya, ya san yadda tsohon shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo ke yekuwar lokaci ya yi da kasashen Afirka za su dawo cikin hayyacinsu, su sama wa kansu tsarin dimokuradiyya mafi dacewa da al’ummominsu.

Obasanjo wanda ake wa kallon masoyin dimokuradiyya tun yana kakin soja bisa yadda ya cika alkawarin dawo da mulki hannun farar hula kamar yadda marigayi Janar Murtala ya kudiri aniyar yi a shekarar 1979, ya ce tabbas dimokuradiyyar Turawan yamma da Afirka ta dauko ba ta kai nahiyar tudun mun tsira ba kuma dama tilasta mana aka yi mu yi aiki da ita daga ‘yan mulkin mallaka, saboda haka ya kamata mu yada kwallon mangwaro mu huta da kuda.
“Dimokuradiyyar Turawan yamma ba ta la’akari da abin da mafi rinjayen al’umma ke so. Tana kafa gwamnati ce ta ‘yan tsiraru a kan jama’a wadanda suke aiki domin ‘yan tsirarun nan ba al’umma gaba daya ba,” don haka ya ba da shawarar a fito da tsarin dimokuradiyya da zai dace da yanayi da tarihi da al’adunmu na Afirka domin mai daki shi ya san wurin da yake masa yoyo.

Duk da cewa, wasu za su ce me ya sa Obasanjon bai yi wannan maganar ba lokacin da ya ci gajiyar dimokuradiyyar a wa’adin mulkinsa daga 1999 zuwa 2007? To, amma ya kamata mu lura cewa, idan dattijo irin Obasanjo ko ma wanda bai kai shi ba ya yi magana, a dubi maganar tukuna da farko a dora ta a sikeli, ta gaskiya ce ko akasinta, sannan mai yiwuwa lokacin da aka samu ilhamar maganar ke nan kuma idan aka yi amfani da ita ba a makara ba.

Turawan yamma sun gama shuka mana lalata tun kafin faduwar katangar Berlin a shekarar 1989, lokacin da suka fito da yekuwar ‘kyakkyawan shugabanci’ na fatar baki a matsayin dabarun ci gaba. A cikin shahararriyar kasidarsa “The End of History”, masanin siyasar Amurka, Francis Fukuyama, ya yi shelar cewa karshen yakin cacar baki shi ne “karshen juyin akidar dan adam da kuma fara samun daukakar dimokuradiyyar yamma mai sassaucin ra’ayi a duniya a matsayin tsarin shugabancin dan adam na karshe.”

Irin wadannan kalamai sun yi nuni da shirye-shiryensu na yin tir da duk wata akida da ta saba wa tasu, don haka ba abin mamaki ba ne, yadda tun a shekarun 1990, bankin duniya ne ya zama mai shata wa Afirka abin da ake nufi da shugabanci na-gari da kuma hanyoyin magance dukkan kalubalen ci gaban da kasashen Afirka ke fuskanta. Wannan ya sa har yanzu duk da muna karni na 21, amma muna dandana kudarmu saboda rashin muhimman abubuwan more rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

Afirka, mun gaji tsarin dimokuradiyya mafi dacewa da al’ummarmu tun kafin zuwan Turawan mulkin mallaka. Misali, a kasar Hausa, sarakuna kan yi nade-naden sarauta daga sassa daban-daban na kasar da suke mulka kamar hakimai, dagatai, masu unguwanni, domin tabbatar da cewa mutanen kowane yanki suna da wakilci a zaman fada da ake yanke hukunce-hukuncen da suka shafi rayuwar al’umma.

Idan kuma a bangaren bai wa mata ‘yanci ne, an san tarihin Sarauniya Daurama (da ake wa take da uwar Hausa Bakwai), ga Sarauniya Amina a Zazzau. Duk wadannan an yi su ne tun kafin zuwan Turawan mulkin mallaka da shekaru masu yawa.

Dimokuradiyya irin ta yamma kuwa ta kasance ta tauye mutane tun fil’azal, kamar yadda wani marubuci, Damola Adejumo-Ayibiowu ya ce a wata makala da ya rubuta aka wallafa a shafin Open Democracy, a shekarar 2019, “Hasali ma, ba a ba wa matan Birtaniya damar kada kuri’a ba sai a shekarar 1928 a lokacin da yawancin matan Afirka, musamman Yarbawa na yammacin Afirka, ke shiga wajen yanke shawara a dama da su a bainar jama’a ba tare da tauye musu hakki ba.”

“Mafi yawan mulkin dimokuradiyya na Yammacin Turai tsari ne na danniya a fakaice cikin al’ummomin da suka zama ‘yan tsiraru. Amma a cikin al’ummomin Afirka kafin mulkin mallaka irin su Igbo, Yarbawa, da Ashanti na Ghana, ana yanke shawara ne yawanci bisa rinjaye (ijma’i), wanda ke tabbatar da cewa an wakilci kowane bangare ta hanyar maslaha domin rage husuma a tsakanin mutane. Abu mafi mahimmanci shi ne, dimokuradiyyar da aka gada daga al’adun Afirka an kafa ce a kan falsafar Afirka ta zamantakewa da kyawawan dabi’unsu. Dimokuradiyya irin ta yammacin duniya kuwa ta samo asali ce daga fafutukar neman ‘yancin kai na magabatanmu wanda aiwatar da ita ta yi illa ga rayuwar talakawa a Afirka.”
Tabbas haka ne, shi ya sa mun kwashe shekaru masu yawa da sunan mulkin ‘yancin kai amma har yau miliyoyin mutanenmu suna fama da kangin talauci sakamakon tsarin shugabancin da aka yaudare mu da shi, baya ga rashin wadatattun ababen more rayuwa.

Amma kuma lokaci bai kure mana ba idan har Afirka za mu farka mu dauki turbar dimokuradiyyar da za ta fi zama mana alheri. Akwai darasin da za mu iya koya daga kasar Sin wadda a shekarar 2007 ne shawarar aiki da “cikakken tsarin dimokuradiyya na bai wa kowa hakkinsa” ya shiga ka’idar siyasar kasar Sin, kuma a yayin babban zaman taro karo na shida na kwamitin koli na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin (CPC) karo na 19 a watan Nuwamban shekarar 2021, aka karfafa manufar. Bayan wata guda kacal, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya fitar da bayanai a kan matakin da aka amince da shi a hukumance mai taken “Sin: Dimokuradiyyar da za ta biya bukata.”

Hakika matukar muna so mu yada kwallon mangwaro mu huta da kuda, wajibi ne shugabanni masu kishin al’umma su amsa irin kiraye-kirayen da su Obasanjo suke yi na kawo tsarin domokuradiyya mafi dacewa da mu a Afirka wanda zai kawo mana sakamakon da kowa zai shaida a fili.

Irin dimokuradiyyar da za ta fifita muradun mutane a kan na kashin kai ko biyan bukatun siyasa, wadda za ta dawo da mu turbar asali ta ci gaban mafi rinjayen mutane ba ‘yan tsiraru ba. Irin wadda za ta fifita cika alkawari ba magana da fatar baki ba.

Za mu iya ganin misalin haka daga dimokuradiyya ta hakika ta kasar Sin wadda ta fitar da mutane miliyan 770 daga kangin talauci a cikin shekaru 40 da suka gabata, tare da kawar da matsanancin talauci baki daya. Ta tabbatar da kiwon lafiya mai inganci da karfin iko ga kusan kashi 20 cikin 100 na al’ummar duniya, kuma ta yi hakan ne a daidai lokacin da wasu suke ganin dimokuradiyyar dake akidarsu ta afka cikin rudani, gazawar shugabanci, tabarbarewar tattalin arziki da karuwar rashin daidaito tare da nau’o’in rikice-rikice na cikin gida da na duniya da ba su yi kama na a zo a gani ba da dimokuradiyya kwata-kwata.

Muna bukatar dimokuradiyyar da za ta kawo mana cin gajiyar juna kamar yadda muke gani a shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kasar Sin ba ta raba kawuna da hada gaba da kakaba takunkumai a tsakanin kasashe kamar yadda Amurka ke yi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaDimokuradiyyaDuniyaKasashen WajeObasanjoShugabanciSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ceto Mutane 3 Daga Wani Gini Da Ya Rushe A Abuja – ‘Yansanda

Next Post

Farashin Man Fetur Ya Kai Naira 937 Kan Kowace Lita A Jigawa 

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

7 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

8 hours ago
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

13 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

17 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

18 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

1 day ago
Next Post
Cire Tallafin Mai Ya Dace, Amma A Gaggauta Saukaka Wa Al’umma

Farashin Man Fetur Ya Kai Naira 937 Kan Kowace Lita A Jigawa 

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.