• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauya Wa Alkalai Wurin Aiki Ba Shi Da Alaka DaShari’ar Nnamdi Kanu – Kotun Daukaka Kara

by Sabo Ahmad
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Sauya Wa Alkalai Wurin Aiki Ba Shi Da Alaka DaShari’ar Nnamdi Kanu – Kotun Daukaka Kara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar kotun daukaka kara da ke Abuja, ta bayyana cewa, sauya wa alkalai 21 wurin aiki a fadin kasar nan ba shi da dangantaka da hukuncin da kotu ta yanke na sakin wadanda ake zargi da ta’addanci a karkashin jagorancin Nnamdi Kanu mai fafutukar kafa kasar Biyafira.

Ba kamar yadda wasu kafafen yada labarai suka bayyana ba, kotun daukaka kara ta ce, sauyawa alkalan 21 daga cikin 81 wani abu ne da aka saba yi domin alkalan su samu kara tabbatar da adalci.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Tsohon Sakataren Gwamnatin Enugu Da Wasu
  • Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

Babban rajistaran kotun, Malam Umar Mohammed Bangari, ya bayyana cewa, labaran da wasu kafofin yada labarai suka bayar na cewa alkalai guda uku da suka yanke hukunci ranar 13, ga watan Okotoba cewa a saki Kanu daga inda ake tsare da shi duk kansu an sauya musu wajen aiki.

Sannan ya ci gaba da cewa, a kashin kansa na babban Rajistara ya ce, alkali daya ne kawai daga cikin alkalai uku da suka yi shari’ar Kanu aka rage masa matsayinsa.

Kamar yadda bayanin ya nuna “An ankarar da kotun daukaka karar kan wani labara da aka buga a jaridar ranar Litinin 24, ga watan Okotoba 2022 mai kanun “Nnamdi Kanu: Alkalai 3 na kotun daukaka kara an sauya musu wajen aiki.”

Labarai Masu Nasaba

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

“A gaskiya, sauya wa alkalai wurin aiki ba sabon abu ba ne, ana yin haka ne domin su kara samun kwarewa”.

Alkalai 21 daga cikin 81wadanda kuma suka hada da wasu alkalan guda 6 wadanda aka sauya wa wajen aiki.

Saboda haka ba gaskiya ba ne a ce, alkalan da suka yi shari’ar Nnamdi Kanu ne suka sa aka sauya wa wasu alkalai wajen aiki ba.

A karshe, muke kira ga wadanda sauyin wurin aikin ya shafa, su ci gaba da rungumar aikinsu da gudanar da shi cikin walwala da kwanciyar hankali, domin tabbatar da adalci ga wadanda suka gurfana a gabansu kamar yadda suka saba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkalaiIPOBKotuNnamdi KanuShari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Guji Yada Kalaman Kiyayya Mai Haddasa Gaba A Tsakanin Al’umma – Dakta Bashir

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindiga A Jigawa 

Related

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

13 minutes ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

4 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

6 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

19 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

1 day ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindiga A Jigawa 

'Yansanda Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindiga A Jigawa 

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

July 2, 2025
Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.