• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

by Sulaiman and Umar Faruk
5 months ago
in Siyasa
0
Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kebbi ta bayyana cewa ta shirya tsaf domin tarbar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Atiku Abubakar, GCON, a ranar 12 ga watan Nuwamba a jihar.

Da yake jawabi ga manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar, Barista Kabiru Tanimu Turaki SAN, mamba a kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP (BOT) ya ce makasudin taron nasu shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararsu na shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar.

  • 2023: Hotunan Atiku Sun Yi Batan-Dabo A Motocin Yakin Neman Zaben PDP A Jihar Ribas

Barista Kabiru Turaki, wanda tsohon ministan ayyuka na musamman ne, ya ce makasudin taron shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararsu na shugaban kasa.

Ya ce: “Abin da za a yi a yau shi ne duba shirye-shiryen karbar dan takararmu na shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, GCON, Wazirin Adamawa, wanda ake sa ran zai ziyarce mu a nan Kebbi a ranar Asabar 12 ga watan Nuwamba, 2022 don gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa ga al’ummar jihar.

Haka kuma, Barista Turaki ya tunatar da cewa ziyarar da Atiku ya kai jihar Kebbi a shekarar 2019 ita ce mafi kyau da aka taba samu a kasar nan, yayin da ya kuma ba da tabbacin jam’iyyar ta kuduri aniyar yiwa maziyartan liyafar da ta dace fiye da ziyarar da ya kawo a baya.

Labarai Masu Nasaba

Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

“Don haka kudurinmu a yau shi ne mu ma mu rubanya adadin mutane, mun zauna mun kafa kwamitocin da za su yi aiki awa 24 daga yanzu har zuwan sa da kuma tafiyarsa a ranakun 12 da 13 ga Nuwamba, 2022.

“Daga nan za mu ziyarci filin wasa na Birnin Kebbi domin duba irin ayyukan da ake yi a can.

“Don haka muna so mu tabbatar wa ‘yan Nijeriya da mambobin kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa cewa shugabancin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi a shirye yake ya karbi dan takararta na shugaban kasa,, a Jihar kebbi, in ji shi”.

Daga karshe, Barista Kabiru Turaki SAN, ya lissafa kwamitocin da suka hada da; babban kwamitin da tsohon Janar Ishaya Bamaiyi zai jagoranta, kwamitin wurin, kwamitin tsaro, kwamitin masauki, kwamitin sufuri, kwamitin nishaɗi da kwamitin yada labarai.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kudin Shigar Kamfanonin Gwamnatin Sin A Rubu’i Uku Na Farkon Bana Ya Karu Da Kaso 10.9 Bisa Dari

Next Post

Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

Related

Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa
Siyasa

Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa

2 days ago
Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa
Siyasa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

2 days ago
‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
Siyasa

‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023

2 days ago
Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC
Siyasa

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

6 days ago
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar
Siyasa

PDP Na Zargin Gwamnan Zamfara Da Yunkurin Murde Sakamakon Karamar Hukumar Maradun

1 week ago
Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ce Sakamakon Zaben Gwamnan Kebbi Bai Kammalu Ba
Siyasa

Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ce Sakamakon Zaben Gwamnan Kebbi Bai Kammalu Ba

1 week ago
Next Post
Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

Xi Jinping Jagoran Sabon Tafarki

LABARAI MASU NASABA

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

Amurka Ta Sake Zargin Kasar Sin Kan Asalin Kwayar Cutar COVID-19 Domin Yunkurin Siyasa

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.