• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shan Maganin Fitar Da Zaƙi Kafin Haihuwa

by Bilkisu Tijjani
8 months ago
Zaki

Yar uwa ki jika abu kaza da kaza ki sha domin ki fitar da zakin dake mararki kafin nakudar haihuwa, ko kuwa wane karbi wannan maganin ka kai wa iyalinka ka ce ta jika ta rika sha maganin zaki ne.

Wadannan su ne irin maganganun da za ka ji suna zagawa musamman tsakanin Mata in sun hadu da mai juna biyu. To amma fa mu a likitance ba mu san wani abu wai shi zaki a marar mace ba ballantana fitarsa a jikin mace mai gabatowar haihuwa.

  • A Rungumi Hakuri A Zaman Aure ‘Yan’uwa Mata
  • NAPTIP Ta Ceto ’Yan Mata 9 Masu Juna Biyu A Abuja

Duk da irin wannan al’ada ta jima amma duk da haka mun shigo wani zamani yanzu da gurbatattun labarai da bayanai marasa sahihanci na ilimi suka yawaita kuma ke kai komo tsakanin al’umma cikin kafafen sadarwa iri-iri.

Komai mutane suka ji ba duk ke tsayawa su yi nazari da binkice ba akan;

Shin kaza din nan da aka ce ya ma dace da ni kuwa?

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

Sannan dadin abin aka fada amma mene ne illar da ka iya biyo bayansa? Shin hakan ma batun yake a ilmance ko kuwa?

Wannan ta sa da zarar haihuwa ta gabatowa mace kowa sai ka ga shawara yake ba ta akan komai ma, musamman ma atsakaninsu mata, Eh munsan kuna yi ne bisa kyakkyawar manufa da son ku ga ta haihu lafiya, amma fa ba duk ‘yan’adam bane zubin halittarsu tare da komai yai daidai da na juna ba.

Ba mamaki wata kuka ji ta yi irin haka ta wanye lafiya, amma mu tuna fa idan wani ya yi abu ya kwana lafiya to fa wani in ya yi wahala zai sha.

Babu wani abu da sunan zaki jikin mai juna biyu, in aka ce zaki a jika to fa mu ko yaushe a likitance abin da muka sani; ana batu ne na ciwon suga ajikin mutum, wato yawaitar sinadarin Bulkodi a cikin jini.

Shi ko ciwon suga yayin goyon ciki, kuma muddin aka gano shi ba’a wata-wata ake dora mace kan shawarwarin abinci ko magunguna wasu lokutan allura domin ba ta kariya daga hatsarin suga da ka iya tasowa, wanda cikin irin wannan hatsarin akwai mutuwar jariri a ciki, mutuwar macen wajen haihuwa, zubewar ciki, ko sanya jariri ya yi girma fiye da kima a ciki ta yadda ba zai iya fitowa ba sai dai ai aiki a ciro shi, ko kuwa sai an kara fadin wajen kafin kan jariri ya iya wucewa.

Wasu kan dauki kowanne katoton jariri lafiya ce tasa, amma ina wani girman ba na ka’ida bane larura ce, galibi alama ce ta larurar suga yayin goyon ciki a uwar musamman a macen da ba ta rika zuwa awo ba, ko kuwa ba ta samu duk gwaje-gwajen da suka dace ba, kurum an auna arziki ne. Duk jaririn da nauyinsa ya wuce kilogiram 3.5 lafiyar mahaifiyarsa abin tuntuba ce a yayin goyon cikinsa.

Shi kuwa wannan sugan ajini yake ba zai taba fita ta ta gaban mace ba ko ta hanyar fitar da wani ruwa ba.

Za Mu Ci Gaba A Mako Mai Zuwa Idan Allah Ya Kai Mu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Labarai

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Next Post
‘Yan Fashin Daji Sun Sace Wasu ‘Yan Jarida Da Mata Da Wasu Yara 2 A Kaduna

‘Yan Bindiga Sun Kashe Wani Mutum Tare Da Sace Mutum Biyu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.