ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Rungumi Hakuri A Zaman Aure ‘Yan’uwa Mata

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
1 year ago
Aure

Hakuri: Yana da matukar riba a rayuwa, ba ma a zamantakewar aure kadai ba, abin da yake damun wasu ma’auratan shi ne gaggawa da rashin hakuri, za ka ga mutum yana fadin cewa yana cikin matsala amma kuma abin mamaki shi ne ba zai iya hakuri akan matsalar ba. Musamman a bangaren mata, ki sani cewa wani abin fa dole take kamawa idan kika kasa hakuri na dan wanin lokaci wallahi hakan sai ya jawo miki shiga matsalar da sai kin dauki tsawon lokaci ba ki fita daga ciki ba.

‘Yar uwa ki yi tunani ki gani lokacin da za’a kawo ki gidanki kowa idan ya gama yi miki huduba abin da yake cike hudubar da shi shi ne a rika hakuri, kada ki yi zaton don su ba su samu soyayyar mijinsu bane (su wadanda suke miki nasihar) a’a wallahi wata a cikinsu soyayyar da mijinta ke gwada mata ke ko rabinta ba za ki samu ba, amma da za ki tambaye ta meye jagoran wannan zaman nasu sai ta ce miki hakuri, haka shima ta bangaren mijin.

  • Zulum Ya Yi Alƙawarin Gyara Sansanin NYSC Na Borno
  • Sin Ta Yi Watsi Da Tsegumin Da Marco Rubio Ya Yi Kan Hadin Gwiwarta Da Latin Amurka

Gidan Mijinki wuri ne wanda kike bakuwa a cikinsa, kin bar inda aka sanki aka san matsalarki, kin je inda ba’a san ko daya daga ciki ba, a da nauyinki ake dauka amma a yanzu dole ke kike daukar nauyin wasu, (wanann shi ne girman) hakuri da kawaici kuma su za su jagorance ki matukar kina son samun sauki a cikin al’amuranki.

ADVERTISEMENT

 

Kada Zakin Soyayya Ya Kwasheki: har ki yi zaton kin tsira daga barazana ko fadan mijinki a’a wallahi sai kin yi hattara ke za ki fi kowa shan fadansa (domin kin fi kowa kusanci da shi) (a halin da kuka kasance a karkashin inuwar aure) matukar ba za ki rinka kiyaye abin da baya so ba.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

Wata ‘yar uwa ana auranta aka kira ta ana yi mata nasiha sai ta ce ni dai kun dame ni da na yi hakuri na yi hakuri, tun da yana sona ina son shi kam ai shike nan, wallahi ko shekara daya ba’a yi ba ran nan na kai mata ziyara sai take cewa Amina ashe da ake cewa na yi hakuri nake ganin an dame ni da gaskiyarsu yanzu wallahi har gani nake hakurin da aka ce na yi ma ya yi kadan.

To rayuwar aure sai da hakuri, idan muka yi hakurin nan da ake fada in sha Allahu za mu ga nasararsa a gaba, amma idan ba mu yi hakurin nan da ake fada mana ba za mu kasance cikin da na sani da damuwa a rayuwarmu. Saboda wasu da zarar auran fari za kufce musu sai ku ga ba za su taba samun nutsuwa ba, ko ga namiji ko macen wanda bai yi hakuri ba a cikin su. Wasu sai ku ga har karshe rayuwarsu ana nadama da da na sani.

Aure
Bilkisu Tijjani
+ posts Bio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Aure
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
Uwargida Sarautar Mata

Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

May 30, 2026
Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
Uwargida Sarautar Mata

Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki

May 24, 2026
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kuskure Goma (10) Da Matan Aure Ke Yi A Gidan Miji

May 16, 2026
Next Post
Xi: Kasar Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da IOC Don Inganta Wasannin Olympic Na Duniya 

Xi: Kasar Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da IOC Don Inganta Wasannin Olympic Na Duniya 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.