• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Ya Kamata A Dauki Batun Makamashi Na Kasashen Afirka Da Muhimmanci Don Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayin Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Ya Kamata A Dauki Batun Makamashi Na Kasashen Afirka Da Muhimmanci Don Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau ne aka rufe taron masu ruwa da tsaki kan yarjejeniyar sauyin yanayi ta MDD karo na 27 (COP27), taron da aka yi shirin kammala shi a ranar 18 ga wata, wanda kuma aka jinkirta shi sakamakon sabanin ra’ayin da bangarori daban daban suka samu ta fannonin tattara kudin biyan tarin asarar da kasashe masu tasowa suka tabka sakamakon sauyin yanayi da ma burin da ake neman cimmawa wajen rage fitar da iskar Carbon.

Sai dai abin farin ciki shi ne, a karshe kasashe daban daban sun cimma daidaito, game da kafa asusun biya hasarorin da aka tabka sakamakon sauyin yanayi, don taimaka wa kasashe masu karamin karfi wajen tinkarar matsalar sauyin yanayin duniya.

  • Masana: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Karfin Afirka A Fannin Aikin Injiniya

Da wuya a cimma daidaito tsakanin kasashe masu ci gaba, musamman Amurka da sauran kasashen yamma, da ma kasashe masu tasowa musamman kasashen Afirka, ta wadannan fannoni biyu, wato tattara kudaden biyan hasarorin da kasashe masu tasowa suka yi sakamakon sauyin yanayi da ma burin da ake neman cimmawa wajen rage fitar da iskar Carbon, sai dai duniyarmu daya ce, kuma “yadda kasashe masu sukuni za su taimaka wa kasashe masu tasowa wajen samun ci gabansu” da ma “yadda kasashe masu ci gaba da kasashe masu tasowa za su dauki mabanbantan nauyi wajen tinkarar sauyin yanayi”, abu ne da ake neman cimmawa wajen daidaita matsalar sauyin yanayi.

Yawan hayaki mai dumama yanayi da kasashen Afirka suka fitar ya kai kaso 4% ne kawai na hayakin da ake fitarwa a duniya baki daya. Matsalar sauyin yanayi ta haddasa musu munanan hasarori, ba laifinsu ba ne, don haka, bai kamata kasashe masu ci gaba su koma gefe suna kallo ba kawai.

A sa’i daya kuma, a baya kasashen Afirka ba su bunkasa sosai ba, kuma hayakin da suke fitarwa bai taka kara ya karya ba. Don haka, a gaba ma bai kamata su dauki nauyi iri daya da na kasashe masu arziki ba.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Kasancewarta ta biyu a duniya ta fannonin fadin filaye da ma yawan al’umma a duniya, nahiyar Afirka na taka muhimmiyar rawa wajen tinkarar sauyin yanayin duniya, don haka ma, ya zama dole a fara taimakawa kasashen Afirka wajen daidaita batun makamashi.

Yawan wutar lantarki da ake amfani da shi a gaba dayan kasar Senegal bai kai yawan wutar lantarki da ake amfani shi a na’urorin wasa na zamani a jihar California ta kasar Amurka ba, kuma kaso 3% na al’ummar kasar Nijeriya suke amfani da na’urar sanyaya daki (Air Conditioner).

A kasashen Afirka da ke kudu da hamadar Sahara, akwai mutane kusan miliyan 600 da suke rayuwa ba tare da samun damar yin amfani da wutar lantarki ba. Ina dalilin haka? Lallai matsalar karancin makamashi da kasashen Afirka ke fuskanta matsala ce ta rashin samun ci gaba. Don haka, muddin dai kasashen Afirka suka tabbatar da ci gabansu da ma damar amfani da makamashi, za su iya samun kwarewar fuskantar sauyin yanayi.

Idan har ana son magance matsalar sauyin yanayi, to, ya zama dole a rage yin amfani da makamashin dake fitar da iskar Carbon. Don haka, a gun taron COP27, kasashe masu arziki sun fi mai da hankali a kan shirin samar da iskar gas na kasashen Afirka, a maimakon matsalar sauyin yanayi da ke addabar kasashen Afirka, har ma sun bukaci kasashen Afirka da su dakatar da yin amfani da albarkatun da suke da su.

Amma abin dariya shi ne a sakamakon rikicin da ya barke tsakanin Rasha da Ukraine, kasashen yamma ko kadan ba su ambaci abin da ya shafi rage iskar Carbon da suke fitarwa ba, har ma suka koma yin amfani da kwal da katako da suke iya kara fitar da iskar Carbon. Kasashen Afirka suna da hakkin raya kansu da ma kyautata rayuwar al’ummarsu, bai kamata wasu kasashe su nuna musu yatsa a kan wannan batu ba, kuma bai kamata su nuna ma’auni biyu ba.

Duk da cewa an cimma daidaito game da kafa asusun biyan hasarorin da aka samu sakamakon sauyin yanayi a gun taron COP27, amma ba a tabbatar da wadanne kasashe ne za su zuba kudaden ba, don haka akwai sauran rina a kaba a fannonin yawan kudaden da za a tara da ma yadda za a raba kudaden.

Duk da haka, muna da imanin cewa, a yayin da ake fuskantar sauyin yanayi, ya kamata kasa da kasa su hada kansu, kuma bai kamata a manta da kasashen Afirka ba, balle ma a bar su a baya ba. (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwargidan Shugaban Nijeriya Aisha Buhari Ta Garzaya Asibiti

Next Post

Mataimakin Shugaban Jami’ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51

Related

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
Daga Birnin Sin

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

18 hours ago
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

19 hours ago
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
Daga Birnin Sin

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

20 hours ago
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

21 hours ago
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

22 hours ago
An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu

23 hours ago
Next Post
Mataimakin Shugaban Jami’ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51

Mataimakin Shugaban Jami'ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51

LABARAI MASU NASABA

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.