ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Jami’ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51

by Muhammad
4 years ago
Mataimakin

Mataimakin shugaban jami’ar jihar Kwara (KWASU), Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN), ya rasu.

Akanbi mai shekaru 51, ya rasu ne a ranar Lahadin da ta gabata a wani asibiti da ke jihar Legas.

  • ‘Yan Bindigar Da Suka Yi Garkuwa Da Malami Da Dansa A Kwara, Sun Bukaci Fansar Miliyan 100
  • EFCC Ta Kama ‘Yan Damfara 18 A Jihar Kwara 

Hukumar jami’ar ta tabbatar da mutuwar Akanbi a wata sanarwa da magatakardar jami’ar, Dokta Kikelomo Sally, ya sanyawa hannu.

ADVERTISEMENT

Kafin a nada shi a matsayin mataimakin shugaban KWASU shekaru biyu da suka wuce, Akanbi malamin shari’a ne a Jami’ar Ilorin (UNILORIN).

“Cikin alhini muna mika wuya ga Allah, Hukumar Gudanarwar Jami’ar Jihar Kwara ta sanar da rasuwar Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN).

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana rashin Akanbi a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da kaduwa da mutuwar tasa.

“Mun mika wuya ga hukuncin Allah wanda yake bayarwa kuma yake karba. A kan wannan muke jimamin rasuwar mataimakin shugaban jami’ar da ya amsa kiran Allah a daren yau. Bawan Allah ne na gaskiya kuma mai kaskantar da kai, muna rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya ba shi Aljannar Firdausi.

“Farfesa a fannin shari’a kwararre ne wanda ya taka rawa wajen bude wani sabon babi na daukaka KWASU. Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa, kai tsaye zuwa ga KWASU da sauran malamai, da ’yan jihar Kwara da ma fadin kasar nan,” in ji gwamnan a wata sanarwa da babban mai yada labaransa ya sanya wa hannu, Rafiu Ajakaye.

A cikin sakon ta’aziyyar Sarkin Ilorin, Alh Ibrahim Sulu-Gambari, ya bayyana alhininsa game da rasuwar Akanbi.

Sulu-Gambari ya bayyana lamarin a matsayin abin ban tsoro, abin bantsoro da damuwa, yana mai jaddada cewa mutuwar Akanbi babban rashi ne ga al’ummar Masarautar Ilorin, Kwara da kuma Jama’a baki daya.

Sakon ta’aziyyar Sarkin na dauke da sa hannun mai magana da yawunsa, Malam Abdulazeez Arowona, ya ce: “Shi (Akanbi) ya kasance kwafin mahaifinsa kuma tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC), Marigayi Mai shari’a Mustapha Akanbi.

Mataimakin
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

July 1, 2026
Next Post
Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.