ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Jami’ar Kwara, Akanbi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 51

by Muhammad
4 years ago
Mataimakin

Mataimakin shugaban jami’ar jihar Kwara (KWASU), Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN), ya rasu.

Akanbi mai shekaru 51, ya rasu ne a ranar Lahadin da ta gabata a wani asibiti da ke jihar Legas.

  • ‘Yan Bindigar Da Suka Yi Garkuwa Da Malami Da Dansa A Kwara, Sun Bukaci Fansar Miliyan 100
  • EFCC Ta Kama ‘Yan Damfara 18 A Jihar Kwara 

Hukumar jami’ar ta tabbatar da mutuwar Akanbi a wata sanarwa da magatakardar jami’ar, Dokta Kikelomo Sally, ya sanyawa hannu.

ADVERTISEMENT

Kafin a nada shi a matsayin mataimakin shugaban KWASU shekaru biyu da suka wuce, Akanbi malamin shari’a ne a Jami’ar Ilorin (UNILORIN).

“Cikin alhini muna mika wuya ga Allah, Hukumar Gudanarwar Jami’ar Jihar Kwara ta sanar da rasuwar Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Muhammed Mustapha Akanbi (SAN).

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana rashin Akanbi a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da kaduwa da mutuwar tasa.

“Mun mika wuya ga hukuncin Allah wanda yake bayarwa kuma yake karba. A kan wannan muke jimamin rasuwar mataimakin shugaban jami’ar da ya amsa kiran Allah a daren yau. Bawan Allah ne na gaskiya kuma mai kaskantar da kai, muna rokon Allah Madaukakin Sarki da Ya ba shi Aljannar Firdausi.

“Farfesa a fannin shari’a kwararre ne wanda ya taka rawa wajen bude wani sabon babi na daukaka KWASU. Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalansa, kai tsaye zuwa ga KWASU da sauran malamai, da ’yan jihar Kwara da ma fadin kasar nan,” in ji gwamnan a wata sanarwa da babban mai yada labaransa ya sanya wa hannu, Rafiu Ajakaye.

A cikin sakon ta’aziyyar Sarkin Ilorin, Alh Ibrahim Sulu-Gambari, ya bayyana alhininsa game da rasuwar Akanbi.

Sulu-Gambari ya bayyana lamarin a matsayin abin ban tsoro, abin bantsoro da damuwa, yana mai jaddada cewa mutuwar Akanbi babban rashi ne ga al’ummar Masarautar Ilorin, Kwara da kuma Jama’a baki daya.

Sakon ta’aziyyar Sarkin na dauke da sa hannun mai magana da yawunsa, Malam Abdulazeez Arowona, ya ce: “Shi (Akanbi) ya kasance kwafin mahaifinsa kuma tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta (ICPC), Marigayi Mai shari’a Mustapha Akanbi.

Mataimakin
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru
Siyasa

Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru

April 25, 2026
Next Post
Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.