• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Al’ummar Kasar Sin Na Sa Ran Rungumar Sabuwar Rayuwa Cikin Sabuwar Shekara

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi:Al’ummar Kasar Sin Na Sa Ran Rungumar Sabuwar Rayuwa Cikin Sabuwar Shekara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, a birnin Beijing da nake zaune, mutane da motoci na kara kai komo a kan tituna kwatankwacin kimanin makwanni biyu zuwa uku da suka wuce.

A wani titin mai yawan gidajen cin abinci a dab da unguwar da nake zama kuma, mutanen da ke zuwa don cin abinci suna ta karuwa, hakan ma kantuna da gidajen sinima da ma sauran wuraren shakatawa.

  • Sin Ta Kiyaye Kokarin Da Take Yi A Baya Da Kuma Nan Gaba

Abin da ke faruwa a birnin Beijing haka ma lamarin yake a sauran sassan kasar Sin, ga dukkan alamu, sakamakon matakan da gwamnati ta dauka na kara kyautata ayyukan kandagarkin cutar Covid-19, al’umma na komawa ga rayuwar da suka saba a baya.

Bisa tushen nasarorin da aka samu wajen kandagarkin cutar Covid-19 cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin kasar Sin ta bullo da jerin matakai na kara kyautata ayyukan kandagarkin cutar Covid-19 tun watan da ya gabata.

A kwanakin baya kuma, ta sanar da sauya matakin yaki da cutar daga rukunin A zuwa rukunin B, wanda za a fara aiwatar da shi tun ranar 8 ga wata mai zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

To, duk wadannan matakai ne da gwamnatin kasar Sin ta dauka bisa la’akari da yanayin cutar da sauran fannoni a kimiyyance, a wani kokari na daidaita aikin kandagarkin cutar da ma bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma, kuma tana daukar matakan ne bisa manufarta ta ainihi, wato dora jama’a a gaban kome.

A hakika, cikin shekaru uku da suka wuce, gwamnatin kasar Sin ta nace ga wannan babbar manufarta ta dora jama’a a gaban kome, inda ta ceton miliyoyin rayukan al’ummar kasar duk da asarorin tattalin arziki da ta fuskanta, ta kuma kiyaye kason mutuwar mutane sakamakon cutar a wani matsayi mafi kankanta a duniya. Mashahurin masanin harkokin kasar Sin na Birtaniya John Ross a tattaunawar da ya yi tare da wakiliyarmu a kwanan baya, ya yi nuni da cewa, kasar Sin ya cimma gaggaruman nasarori wajen kiyaye lafiyar al’ummarta da kuma ceton rayukansu. Ya ce, “Sama da mutane miliyan daya cutar ta halaka a kasar Amurka, idan aka kwatanta wannan kaso na mutuwa a kasar Sin, lallai yawan mamata sakamakon cutar a kasar ka iya kaiwa sama da miliyan 4.6. Don haka, muna iya cewa gwamnatin kasar Sin ta ceto rayukan mutane sama da miliyan 4.”

Ta hanyar daukar tsauraran matakai masu inganci wajen kandagarkin cutar, kasar Sin ta samu isasshen lokaci na nazarin magunguna da samar da rigakafi cikin shekaru uku da suka wuce, a yayin da cutar Covid-19 ma ta yi ta sauyawa zuwa nau’in Omicron wadda ta kara karfin yaduwa amma irin barnar da take haifarwa ga lafiyar mutum ba ta kai ta ainihin cutar ba, inda yawan wadanda suka harbu da cutar da ke nuna alamu masu tsanani da wadanda cutar ta halaka duk sun ragu kwarai da gaske.

Wannan ya sa, gwamnatin kasar Sin ta daidaita matakanta na kandagarkin cutar. A sa’i daya kuma, kasar ta yi wa akasarin al’ummarta cikakken rigakafi, ta kuma tara dimbin fasahohi na yaki da cutar, tare da inganta aikin nazarin magunguna da kiwon lafiya, matakan da suka aza harsashi mai inganci ga kyautata ayyukan kandagarkin cutar.

Ba shakka, duk kasar da ta sassauta matakan kandagarkin cutar, za ta samu saurin karuwar masu cutar da ma wasu matsaloli ta fannin kiwon lafiya na dan gajeren lokaci, abin da kasar Sin ma take fuskanta ke nan a sakamakon daidaita matakanta, sai dai hakan ya zama dalilin da wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma ke zargin kasar da su, abin dariya shi ne, a baya, wadannan kafofi ne suke zargin kasar Sin da daukar matakan kandagarki fiye da kima. Don haka, matsalar ba wai ita ce me kasar Sin ta yi, sabo da sukar kasar shi ne abin da ya dace ga kasashen ta fannin siyasa.

Ni kaina tare da wasu iyalaina da abokaina a kwanakin baya ma mun harbu da cutar, sai dai akasarinmu ba mu nuna wata alamar cutar ba ko kuma alamu masu sauki ne muka nuna, kuma bayan kimanin sama da mako daya da muka killace kanmu a gida mu ka huta, sai mu ka warke kuma mu ka koma bakin aiki da ma rayuwar da muka saba.

’Yan kwanaki kadan suka rag a shiga wata sabuwar shekara, gwamnatin kasar Sin yanzu na kokarin daukar matakai don daidaita matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu, kuma al’ummar kasar ma na sa ran rungumar sabuwar rayuwarsu a cikin sabuwar shekara. (Lubabatu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Zan Dora Daga Inda Na Tsaya Idan Na Zarce – Matawalle

Next Post

An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

16 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

16 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

18 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

19 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Kwato Makamai 

An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.