• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Al’ummar Kasar Sin Na Sa Ran Rungumar Sabuwar Rayuwa Cikin Sabuwar Shekara

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi:Al’ummar Kasar Sin Na Sa Ran Rungumar Sabuwar Rayuwa Cikin Sabuwar Shekara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, a birnin Beijing da nake zaune, mutane da motoci na kara kai komo a kan tituna kwatankwacin kimanin makwanni biyu zuwa uku da suka wuce.

A wani titin mai yawan gidajen cin abinci a dab da unguwar da nake zama kuma, mutanen da ke zuwa don cin abinci suna ta karuwa, hakan ma kantuna da gidajen sinima da ma sauran wuraren shakatawa.

  • Sin Ta Kiyaye Kokarin Da Take Yi A Baya Da Kuma Nan Gaba

Abin da ke faruwa a birnin Beijing haka ma lamarin yake a sauran sassan kasar Sin, ga dukkan alamu, sakamakon matakan da gwamnati ta dauka na kara kyautata ayyukan kandagarkin cutar Covid-19, al’umma na komawa ga rayuwar da suka saba a baya.

Bisa tushen nasarorin da aka samu wajen kandagarkin cutar Covid-19 cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin kasar Sin ta bullo da jerin matakai na kara kyautata ayyukan kandagarkin cutar Covid-19 tun watan da ya gabata.

A kwanakin baya kuma, ta sanar da sauya matakin yaki da cutar daga rukunin A zuwa rukunin B, wanda za a fara aiwatar da shi tun ranar 8 ga wata mai zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

To, duk wadannan matakai ne da gwamnatin kasar Sin ta dauka bisa la’akari da yanayin cutar da sauran fannoni a kimiyyance, a wani kokari na daidaita aikin kandagarkin cutar da ma bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma, kuma tana daukar matakan ne bisa manufarta ta ainihi, wato dora jama’a a gaban kome.

A hakika, cikin shekaru uku da suka wuce, gwamnatin kasar Sin ta nace ga wannan babbar manufarta ta dora jama’a a gaban kome, inda ta ceton miliyoyin rayukan al’ummar kasar duk da asarorin tattalin arziki da ta fuskanta, ta kuma kiyaye kason mutuwar mutane sakamakon cutar a wani matsayi mafi kankanta a duniya. Mashahurin masanin harkokin kasar Sin na Birtaniya John Ross a tattaunawar da ya yi tare da wakiliyarmu a kwanan baya, ya yi nuni da cewa, kasar Sin ya cimma gaggaruman nasarori wajen kiyaye lafiyar al’ummarta da kuma ceton rayukansu. Ya ce, “Sama da mutane miliyan daya cutar ta halaka a kasar Amurka, idan aka kwatanta wannan kaso na mutuwa a kasar Sin, lallai yawan mamata sakamakon cutar a kasar ka iya kaiwa sama da miliyan 4.6. Don haka, muna iya cewa gwamnatin kasar Sin ta ceto rayukan mutane sama da miliyan 4.”

Ta hanyar daukar tsauraran matakai masu inganci wajen kandagarkin cutar, kasar Sin ta samu isasshen lokaci na nazarin magunguna da samar da rigakafi cikin shekaru uku da suka wuce, a yayin da cutar Covid-19 ma ta yi ta sauyawa zuwa nau’in Omicron wadda ta kara karfin yaduwa amma irin barnar da take haifarwa ga lafiyar mutum ba ta kai ta ainihin cutar ba, inda yawan wadanda suka harbu da cutar da ke nuna alamu masu tsanani da wadanda cutar ta halaka duk sun ragu kwarai da gaske.

Wannan ya sa, gwamnatin kasar Sin ta daidaita matakanta na kandagarkin cutar. A sa’i daya kuma, kasar ta yi wa akasarin al’ummarta cikakken rigakafi, ta kuma tara dimbin fasahohi na yaki da cutar, tare da inganta aikin nazarin magunguna da kiwon lafiya, matakan da suka aza harsashi mai inganci ga kyautata ayyukan kandagarkin cutar.

Ba shakka, duk kasar da ta sassauta matakan kandagarkin cutar, za ta samu saurin karuwar masu cutar da ma wasu matsaloli ta fannin kiwon lafiya na dan gajeren lokaci, abin da kasar Sin ma take fuskanta ke nan a sakamakon daidaita matakanta, sai dai hakan ya zama dalilin da wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma ke zargin kasar da su, abin dariya shi ne, a baya, wadannan kafofi ne suke zargin kasar Sin da daukar matakan kandagarki fiye da kima. Don haka, matsalar ba wai ita ce me kasar Sin ta yi, sabo da sukar kasar shi ne abin da ya dace ga kasashen ta fannin siyasa.

Ni kaina tare da wasu iyalaina da abokaina a kwanakin baya ma mun harbu da cutar, sai dai akasarinmu ba mu nuna wata alamar cutar ba ko kuma alamu masu sauki ne muka nuna, kuma bayan kimanin sama da mako daya da muka killace kanmu a gida mu ka huta, sai mu ka warke kuma mu ka koma bakin aiki da ma rayuwar da muka saba.

’Yan kwanaki kadan suka rag a shiga wata sabuwar shekara, gwamnatin kasar Sin yanzu na kokarin daukar matakai don daidaita matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu, kuma al’ummar kasar ma na sa ran rungumar sabuwar rayuwarsu a cikin sabuwar shekara. (Lubabatu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Zan Dora Daga Inda Na Tsaya Idan Na Zarce – Matawalle

Next Post

An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka

Related

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

18 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

19 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

20 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

22 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

23 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Kwato Makamai 

An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka

LABARAI MASU NASABA

Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.