ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Al’ummar Kasar Sin Na Sa Ran Rungumar Sabuwar Rayuwa Cikin Sabuwar Shekara

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Kwanan nan, a birnin Beijing da nake zaune, mutane da motoci na kara kai komo a kan tituna kwatankwacin kimanin makwanni biyu zuwa uku da suka wuce.

A wani titin mai yawan gidajen cin abinci a dab da unguwar da nake zama kuma, mutanen da ke zuwa don cin abinci suna ta karuwa, hakan ma kantuna da gidajen sinima da ma sauran wuraren shakatawa.

  • Sin Ta Kiyaye Kokarin Da Take Yi A Baya Da Kuma Nan Gaba

Abin da ke faruwa a birnin Beijing haka ma lamarin yake a sauran sassan kasar Sin, ga dukkan alamu, sakamakon matakan da gwamnati ta dauka na kara kyautata ayyukan kandagarkin cutar Covid-19, al’umma na komawa ga rayuwar da suka saba a baya.

ADVERTISEMENT

Bisa tushen nasarorin da aka samu wajen kandagarkin cutar Covid-19 cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin kasar Sin ta bullo da jerin matakai na kara kyautata ayyukan kandagarkin cutar Covid-19 tun watan da ya gabata.

A kwanakin baya kuma, ta sanar da sauya matakin yaki da cutar daga rukunin A zuwa rukunin B, wanda za a fara aiwatar da shi tun ranar 8 ga wata mai zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

To, duk wadannan matakai ne da gwamnatin kasar Sin ta dauka bisa la’akari da yanayin cutar da sauran fannoni a kimiyyance, a wani kokari na daidaita aikin kandagarkin cutar da ma bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma, kuma tana daukar matakan ne bisa manufarta ta ainihi, wato dora jama’a a gaban kome.

A hakika, cikin shekaru uku da suka wuce, gwamnatin kasar Sin ta nace ga wannan babbar manufarta ta dora jama’a a gaban kome, inda ta ceton miliyoyin rayukan al’ummar kasar duk da asarorin tattalin arziki da ta fuskanta, ta kuma kiyaye kason mutuwar mutane sakamakon cutar a wani matsayi mafi kankanta a duniya. Mashahurin masanin harkokin kasar Sin na Birtaniya John Ross a tattaunawar da ya yi tare da wakiliyarmu a kwanan baya, ya yi nuni da cewa, kasar Sin ya cimma gaggaruman nasarori wajen kiyaye lafiyar al’ummarta da kuma ceton rayukansu. Ya ce, “Sama da mutane miliyan daya cutar ta halaka a kasar Amurka, idan aka kwatanta wannan kaso na mutuwa a kasar Sin, lallai yawan mamata sakamakon cutar a kasar ka iya kaiwa sama da miliyan 4.6. Don haka, muna iya cewa gwamnatin kasar Sin ta ceto rayukan mutane sama da miliyan 4.”

Ta hanyar daukar tsauraran matakai masu inganci wajen kandagarkin cutar, kasar Sin ta samu isasshen lokaci na nazarin magunguna da samar da rigakafi cikin shekaru uku da suka wuce, a yayin da cutar Covid-19 ma ta yi ta sauyawa zuwa nau’in Omicron wadda ta kara karfin yaduwa amma irin barnar da take haifarwa ga lafiyar mutum ba ta kai ta ainihin cutar ba, inda yawan wadanda suka harbu da cutar da ke nuna alamu masu tsanani da wadanda cutar ta halaka duk sun ragu kwarai da gaske.

Wannan ya sa, gwamnatin kasar Sin ta daidaita matakanta na kandagarkin cutar. A sa’i daya kuma, kasar ta yi wa akasarin al’ummarta cikakken rigakafi, ta kuma tara dimbin fasahohi na yaki da cutar, tare da inganta aikin nazarin magunguna da kiwon lafiya, matakan da suka aza harsashi mai inganci ga kyautata ayyukan kandagarkin cutar.

Ba shakka, duk kasar da ta sassauta matakan kandagarkin cutar, za ta samu saurin karuwar masu cutar da ma wasu matsaloli ta fannin kiwon lafiya na dan gajeren lokaci, abin da kasar Sin ma take fuskanta ke nan a sakamakon daidaita matakanta, sai dai hakan ya zama dalilin da wasu kafofin yada labarai na kasashen yamma ke zargin kasar da su, abin dariya shi ne, a baya, wadannan kafofi ne suke zargin kasar Sin da daukar matakan kandagarki fiye da kima. Don haka, matsalar ba wai ita ce me kasar Sin ta yi, sabo da sukar kasar shi ne abin da ya dace ga kasashen ta fannin siyasa.

Ni kaina tare da wasu iyalaina da abokaina a kwanakin baya ma mun harbu da cutar, sai dai akasarinmu ba mu nuna wata alamar cutar ba ko kuma alamu masu sauki ne muka nuna, kuma bayan kimanin sama da mako daya da muka killace kanmu a gida mu ka huta, sai mu ka warke kuma mu ka koma bakin aiki da ma rayuwar da muka saba.

’Yan kwanaki kadan suka rag a shiga wata sabuwar shekara, gwamnatin kasar Sin yanzu na kokarin daukar matakai don daidaita matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu, kuma al’ummar kasar ma na sa ran rungumar sabuwar rayuwarsu a cikin sabuwar shekara. (Lubabatu)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Kwato Makamai 

An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.