• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Tarkon Bashi Ne Ko Kuma Na Yaudara?

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi:Tarkon Bashi Ne Ko Kuma Na Yaudara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A sakamakon komadar tattalin arzikin duniya, da kuma faduwar farashin mai da na sauran kayayyaki a fadin duniya cikin ‘yan shekarun baya, kudin shigar kasashen Afirka ya ragu, lamarin da ya haifar da matsalar bashi gare su, baya ga kuma annobar Covid-19 da ta yi ta addabar duniya, wadda ta kara tsananta matsalar.

Ganin haka ya sa kasashen yammacin duniya suke ta yayata zancen wai “tarkon bashin kasar Sin” , tamkar kasar Sin ce tafi kowa bin kasashen Afirka basussuka, wadda kuma take daukar alhakin matsalar da suke fuskanta.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

Sai dai alkaluma ba su karya. Wani rahoton da cibiyar nazari ta “Debt Justice” ta kasar Birtaniya, ta fitar a kwanan baya ya yi nuni da cewa, bisa ga kididdigar da bankin duniya ya yi, daga cikin basussukan da gwamnatocin kasashen Afirka suka ci, kaso 12% na kasar Sin ne, a yayin da kasashen yamma, musamman ma sassa masu zaman kansu suke binsu kaso 35%.

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta samar da basussuka ne kan kudin ruwan da ya kai kaso 2.7%, a yayin da kudin ruwan da kasashen yamma suke karba ya kai kaso 5%. Lallai kamar yadda Tim Jones, babban jami’in cibiyar ta “Debt Justice” ya fada, “shugabannin kasashen yamma suna dora laifin matsalar bashi kan kasar Sin ne, don kawar da idon al’umma.

A hakika, bankuna da kamfanonin kula da jari da na cinikin mai nasu sun fi daukar alhakin.”
Ban da haka kuma, Sin da kasashen Afirka sun sha bamban sosai, duk da cewa dukkansu na bin kasashen Afirka basussuka.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Na farko, burin da suke neman cimmawa ba daya ba ne. Kasar Sin ta fi mai da hankali a kan bunkasuwar kasashen Afirka cikin dogon lokaci a yayin da take samar musu basussuka, don haka, ta fi samar da basussukan fannonin kere-kere, da ma manyan ababen more rayuwa, har ma ribar da hakan ya samar tuni ta zarce basussukan, a yayin da kasashen yamma suka kasa sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikin Afirka, har ma sun sa su kara shiga kangin talauci, kuma hakan suke ta kara neman basussuka daga wajensu.

Na biyu kuma, kasar Sin na aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka ne bisa zaman daidaito, ba tare da tsoma baki cikin harkokin gidansu, don haka ma, ba ta taba gindaya sharudan siyasa ba a yayin da take bin su basussuka, kwatankwacin yadda kasashen yamma su kan gindaya sharudan siyasa, da suka shafi hakkin bil Adam, da gyare-gyaren dokoki da makamantansu, a yunkurin tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen bisa ga basussukan da suka samar.

Na uku, kullum kasar Sin na dora muhimmanci a kan saukaka wa kasashen Afirka matsalar basussuka. A tarukan dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka(FOCAC) , ta sha soke basussuka maras ruwa da take bin gwamnatocin kasashen Afirka, da suke matukar fama da matsalar bashi wadanda suka kasa biya, baya ga kuma yadda take kokarin shiga hadin gwiwar sassa daban daban kan batun bashi, har ma ta zamanto ta farko wajen yawan basussukan da ta tsawaita wa’adin biyansu daga cikin kasashen G20, kwatankwacin yadda kasashen yamma suka yi shiru game da batun tsawaita wa’adin basussukan nasu sassa masu zaman kansu ke bin kasashe mafiya fama da talauci, baya ga kuma yadda suke yayata zancen wai “tarkon bashin kasar Sin” a kungiyar G7.

Da haka muke iya gano cewa, maganar wai “tarkon bashin kasar Sin”, tarko ne kasashen yamma suka kafa don hana kasashen Afirka samun ci gaba, haka kuma yaudara ce ta lalata hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. (Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

De Ligt Ya Koma Bayern Munchen Daga Juventus

Next Post

Wata Mata Ta Kashe Mijinta Da Wuka Har Lahira A Adamawa

Related

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

10 hours ago
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika
Daga Birnin Sin

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

11 hours ago
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

12 hours ago
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

13 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

14 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

15 hours ago
Next Post
Wata Mata Ta Kashe Mijinta Da Wuka Har Lahira A Adamawa

Wata Mata Ta Kashe Mijinta Da Wuka Har Lahira A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.