• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Tarkon Bashi Ne Ko Kuma Na Yaudara?

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi:Tarkon Bashi Ne Ko Kuma Na Yaudara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A sakamakon komadar tattalin arzikin duniya, da kuma faduwar farashin mai da na sauran kayayyaki a fadin duniya cikin ‘yan shekarun baya, kudin shigar kasashen Afirka ya ragu, lamarin da ya haifar da matsalar bashi gare su, baya ga kuma annobar Covid-19 da ta yi ta addabar duniya, wadda ta kara tsananta matsalar.

Ganin haka ya sa kasashen yammacin duniya suke ta yayata zancen wai “tarkon bashin kasar Sin” , tamkar kasar Sin ce tafi kowa bin kasashen Afirka basussuka, wadda kuma take daukar alhakin matsalar da suke fuskanta.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

Sai dai alkaluma ba su karya. Wani rahoton da cibiyar nazari ta “Debt Justice” ta kasar Birtaniya, ta fitar a kwanan baya ya yi nuni da cewa, bisa ga kididdigar da bankin duniya ya yi, daga cikin basussukan da gwamnatocin kasashen Afirka suka ci, kaso 12% na kasar Sin ne, a yayin da kasashen yamma, musamman ma sassa masu zaman kansu suke binsu kaso 35%.

A sa’i daya kuma, kasar Sin ta samar da basussuka ne kan kudin ruwan da ya kai kaso 2.7%, a yayin da kudin ruwan da kasashen yamma suke karba ya kai kaso 5%. Lallai kamar yadda Tim Jones, babban jami’in cibiyar ta “Debt Justice” ya fada, “shugabannin kasashen yamma suna dora laifin matsalar bashi kan kasar Sin ne, don kawar da idon al’umma.

A hakika, bankuna da kamfanonin kula da jari da na cinikin mai nasu sun fi daukar alhakin.”
Ban da haka kuma, Sin da kasashen Afirka sun sha bamban sosai, duk da cewa dukkansu na bin kasashen Afirka basussuka.

Labarai Masu Nasaba

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Na farko, burin da suke neman cimmawa ba daya ba ne. Kasar Sin ta fi mai da hankali a kan bunkasuwar kasashen Afirka cikin dogon lokaci a yayin da take samar musu basussuka, don haka, ta fi samar da basussukan fannonin kere-kere, da ma manyan ababen more rayuwa, har ma ribar da hakan ya samar tuni ta zarce basussukan, a yayin da kasashen yamma suka kasa sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikin Afirka, har ma sun sa su kara shiga kangin talauci, kuma hakan suke ta kara neman basussuka daga wajensu.

Na biyu kuma, kasar Sin na aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka ne bisa zaman daidaito, ba tare da tsoma baki cikin harkokin gidansu, don haka ma, ba ta taba gindaya sharudan siyasa ba a yayin da take bin su basussuka, kwatankwacin yadda kasashen yamma su kan gindaya sharudan siyasa, da suka shafi hakkin bil Adam, da gyare-gyaren dokoki da makamantansu, a yunkurin tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen bisa ga basussukan da suka samar.

Na uku, kullum kasar Sin na dora muhimmanci a kan saukaka wa kasashen Afirka matsalar basussuka. A tarukan dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka(FOCAC) , ta sha soke basussuka maras ruwa da take bin gwamnatocin kasashen Afirka, da suke matukar fama da matsalar bashi wadanda suka kasa biya, baya ga kuma yadda take kokarin shiga hadin gwiwar sassa daban daban kan batun bashi, har ma ta zamanto ta farko wajen yawan basussukan da ta tsawaita wa’adin biyansu daga cikin kasashen G20, kwatankwacin yadda kasashen yamma suka yi shiru game da batun tsawaita wa’adin basussukan nasu sassa masu zaman kansu ke bin kasashe mafiya fama da talauci, baya ga kuma yadda suke yayata zancen wai “tarkon bashin kasar Sin” a kungiyar G7.

Da haka muke iya gano cewa, maganar wai “tarkon bashin kasar Sin”, tarko ne kasashen yamma suka kafa don hana kasashen Afirka samun ci gaba, haka kuma yaudara ce ta lalata hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. (Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

De Ligt Ya Koma Bayern Munchen Daga Juventus

Next Post

Wata Mata Ta Kashe Mijinta Da Wuka Har Lahira A Adamawa

Related

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

4 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

5 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

6 hours ago
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
Daga Birnin Sin

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

7 hours ago
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Daga Birnin Sin

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

7 hours ago
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 
Daga Birnin Sin

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

8 hours ago
Next Post
Wata Mata Ta Kashe Mijinta Da Wuka Har Lahira A Adamawa

Wata Mata Ta Kashe Mijinta Da Wuka Har Lahira A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.