• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Siyasa
0
Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar zabe a jihar Katsina Alhaji Jibrin Ibrahim Zarewa, ya ba da tabbacin hada karfe da karfe da kungiyar darika awareness forum, wajan ci gaba da wayar da kan jama’a a kan abin da ya shafi hukumar zabe da kuma rijistar katin zabe da ake gudanarwa a fadin Nijeriya.

Zarewa ya bayyana haka a lokacin da shuwagabannin kungiyar suka kai masa ziyara a shalkwatar hukumar da ke Katsina.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa
  • ‘Yan Sanda Da ‘Yan Kasuwa Sun Yi Hadin Guiwa Don Kawo Karshen Kwacen Waya A Kano

Tunda farko dai shugaban ya yi wa tawagar kungiyar cikakken bayani game da ita kanta hukumar zabe da kuma irin ayyukan da doka ta sahale mata ta yi akan fannoni daban-daban.

Ya kuma nuna jin dadinsa da ziyarar  tare da fadin cewa INEC a shirye take ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar, musamman a kan abinbda ya shafi wayar da kan jama’a kan batun katin zabe da sauran batutuwa a fadin jihar Katsina.

Haka kuma Zarewa, ya ce wannan ziyara an yi ta a lokacin da ya da ce, duk da cewa wuri ya kure amma dai kungiyar na da rawar da zata taka wajen ganin an kara samun narasa.

Labarai Masu Nasaba

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

“Wani abu da ba ku sani ba shi ne, an yi wa jihar Katsina nisa wajen yin rijistar katin zabe, idan aka duba matsayin jihar Katsina ta hudu a yawan mutane da masu katin zaɓe, amma yanzu ta koma ta ashirin da hudu, wanda ba haka muka so ba” inji shi

Kazalika ya yi dogon bayani a kan yadda suka samu karin rumfunan zabe da wuraren da aka kai su, tare da daukar alkawarin cewa duk lokacin da hukumar za ta yi wani taro na masu ruwa da tsaki kungiyar na cikin sahun gaba saboda muhimmanci da irin tsare-tsaren da suke da shi.

Tunda da farko da yake nasa jawabin a kan makasudin wannan ziyara ta su, shugaban tafiyar kuma daya daga cikin kwamitin amintattu na kungiyar, Farfesa Abdulaziz Ahmad Mashi, ya bayyana cewa tuni suka so kawo ziyara amma yanzu Allah baya kaddara hakan.

Ya kara da cewa suna son hada gwuiwa da hukumar zabe domin ba da ta su gudunmawar wajen ganin jama’a sun yanki katin zabe kuma kungiyarsu ba ta da alaka ta nesa ko ta kusa da kowace irin jam’iyyar siyasa.

Farfesa Mashi, ya ce bisa haka ne suke neman cikakken bayani game da ayyukan wannan hukuma wanda hakan zai ba su damar sanin ta inda za su ba da gudunmawa ganin cewa mafi yawansu a tafiyar matasa ne.

Sannan ya nemi hukumar zabe da ta dauki kungiyar a matsayin abokiyar tafiya wajen isar da sako ga al’ummar Musulmi ba wai sai ‘yan darika kawai ba.

A nasa ta’alikin sakataren tsare -tsaren kungiyar, Awwal Abba Yahaya, ya ba da tarihin kafuwar kungiyar da kuma dalilin da ya sa aka kafa ta tare da yin bayanin irin tsarin shugabancin da suke da shi a matakin jiha da shiyya da kananan hukumomi zuwa mazabu.

Abba ya ce suna amfani da hanya mafi sauki wajen isar da kowane irin sako ake son isarwa ga mambobinsu, ko dai ta hanyar haduwa a Masallatai na yau da kullum ko kuma duk sati wajen zikirin Juma’a.

“Kimanin shekaru bakwai ke nan da kafa wannan kungiya wanda take da wakilin kowane bangare a darika kuma muna da shugabanni tun daga matakin jiha da shiyya da kuma kananan hukumomi, har da matakin rumfa, kuma babu ruwanmu da wata jam’iyyar siyasa, muna yin wanna tafiya ne ganin yadda aka bar mu a baya akan batun siyasa amma yanzu mun farka kuma za a damu da mu” inji shi

Daga karshe sakataran tsare-tsaren, ya ce sun shirya tsaf domin ci gaba da wayar da jama’a a kan wannan hidima ta katin zabe, inda ya ce za su yi amfani da kafafen yada labarai wajen isar da sakon, tare da ba da tabbacin za a ga canji nan kusa ba nesa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Darika Awareness Forum KatsinaINECKada Kuri'aKatin ZabeSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa

Next Post

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Related

Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 days ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

5 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

5 days ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 days ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Siyasa

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

1 week ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

1 week ago
Next Post
Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

July 16, 2025
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

July 16, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

July 16, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

July 16, 2025
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

July 16, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.