ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe a jihar Katsina Alhaji Jibrin Ibrahim Zarewa, ya ba da tabbacin hada karfe da karfe da kungiyar darika awareness forum, wajan ci gaba da wayar da kan jama’a a kan abin da ya shafi hukumar zabe da kuma rijistar katin zabe da ake gudanarwa a fadin Nijeriya.

Zarewa ya bayyana haka a lokacin da shuwagabannin kungiyar suka kai masa ziyara a shalkwatar hukumar da ke Katsina.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa
  • ‘Yan Sanda Da ‘Yan Kasuwa Sun Yi Hadin Guiwa Don Kawo Karshen Kwacen Waya A Kano

Tunda farko dai shugaban ya yi wa tawagar kungiyar cikakken bayani game da ita kanta hukumar zabe da kuma irin ayyukan da doka ta sahale mata ta yi akan fannoni daban-daban.

ADVERTISEMENT

Ya kuma nuna jin dadinsa da ziyarar  tare da fadin cewa INEC a shirye take ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar, musamman a kan abinbda ya shafi wayar da kan jama’a kan batun katin zabe da sauran batutuwa a fadin jihar Katsina.

Haka kuma Zarewa, ya ce wannan ziyara an yi ta a lokacin da ya da ce, duk da cewa wuri ya kure amma dai kungiyar na da rawar da zata taka wajen ganin an kara samun narasa.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Wani abu da ba ku sani ba shi ne, an yi wa jihar Katsina nisa wajen yin rijistar katin zabe, idan aka duba matsayin jihar Katsina ta hudu a yawan mutane da masu katin zaɓe, amma yanzu ta koma ta ashirin da hudu, wanda ba haka muka so ba” inji shi

Kazalika ya yi dogon bayani a kan yadda suka samu karin rumfunan zabe da wuraren da aka kai su, tare da daukar alkawarin cewa duk lokacin da hukumar za ta yi wani taro na masu ruwa da tsaki kungiyar na cikin sahun gaba saboda muhimmanci da irin tsare-tsaren da suke da shi.

Tunda da farko da yake nasa jawabin a kan makasudin wannan ziyara ta su, shugaban tafiyar kuma daya daga cikin kwamitin amintattu na kungiyar, Farfesa Abdulaziz Ahmad Mashi, ya bayyana cewa tuni suka so kawo ziyara amma yanzu Allah baya kaddara hakan.

Ya kara da cewa suna son hada gwuiwa da hukumar zabe domin ba da ta su gudunmawar wajen ganin jama’a sun yanki katin zabe kuma kungiyarsu ba ta da alaka ta nesa ko ta kusa da kowace irin jam’iyyar siyasa.

Farfesa Mashi, ya ce bisa haka ne suke neman cikakken bayani game da ayyukan wannan hukuma wanda hakan zai ba su damar sanin ta inda za su ba da gudunmawa ganin cewa mafi yawansu a tafiyar matasa ne.

Sannan ya nemi hukumar zabe da ta dauki kungiyar a matsayin abokiyar tafiya wajen isar da sako ga al’ummar Musulmi ba wai sai ‘yan darika kawai ba.

A nasa ta’alikin sakataren tsare -tsaren kungiyar, Awwal Abba Yahaya, ya ba da tarihin kafuwar kungiyar da kuma dalilin da ya sa aka kafa ta tare da yin bayanin irin tsarin shugabancin da suke da shi a matakin jiha da shiyya da kananan hukumomi zuwa mazabu.

Abba ya ce suna amfani da hanya mafi sauki wajen isar da kowane irin sako ake son isarwa ga mambobinsu, ko dai ta hanyar haduwa a Masallatai na yau da kullum ko kuma duk sati wajen zikirin Juma’a.

“Kimanin shekaru bakwai ke nan da kafa wannan kungiya wanda take da wakilin kowane bangare a darika kuma muna da shugabanni tun daga matakin jiha da shiyya da kuma kananan hukumomi, har da matakin rumfa, kuma babu ruwanmu da wata jam’iyyar siyasa, muna yin wanna tafiya ne ganin yadda aka bar mu a baya akan batun siyasa amma yanzu mun farka kuma za a damu da mu” inji shi

Daga karshe sakataran tsare-tsaren, ya ce sun shirya tsaf domin ci gaba da wayar da jama’a a kan wannan hidima ta katin zabe, inda ya ce za su yi amfani da kafafen yada labarai wajen isar da sakon, tare da ba da tabbacin za a ga canji nan kusa ba nesa ba.

INEC
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.