ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
INEC

Shugaban hukumar zabe a jihar Katsina Alhaji Jibrin Ibrahim Zarewa, ya ba da tabbacin hada karfe da karfe da kungiyar darika awareness forum, wajan ci gaba da wayar da kan jama’a a kan abin da ya shafi hukumar zabe da kuma rijistar katin zabe da ake gudanarwa a fadin Nijeriya.

Zarewa ya bayyana haka a lokacin da shuwagabannin kungiyar suka kai masa ziyara a shalkwatar hukumar da ke Katsina.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kansila A Adamawa
  • ‘Yan Sanda Da ‘Yan Kasuwa Sun Yi Hadin Guiwa Don Kawo Karshen Kwacen Waya A Kano

Tunda farko dai shugaban ya yi wa tawagar kungiyar cikakken bayani game da ita kanta hukumar zabe da kuma irin ayyukan da doka ta sahale mata ta yi akan fannoni daban-daban.

ADVERTISEMENT

Ya kuma nuna jin dadinsa da ziyarar  tare da fadin cewa INEC a shirye take ta yi aiki kafada da kafada da kungiyar, musamman a kan abinbda ya shafi wayar da kan jama’a kan batun katin zabe da sauran batutuwa a fadin jihar Katsina.

Haka kuma Zarewa, ya ce wannan ziyara an yi ta a lokacin da ya da ce, duk da cewa wuri ya kure amma dai kungiyar na da rawar da zata taka wajen ganin an kara samun narasa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Wani abu da ba ku sani ba shi ne, an yi wa jihar Katsina nisa wajen yin rijistar katin zabe, idan aka duba matsayin jihar Katsina ta hudu a yawan mutane da masu katin zaɓe, amma yanzu ta koma ta ashirin da hudu, wanda ba haka muka so ba” inji shi

Kazalika ya yi dogon bayani a kan yadda suka samu karin rumfunan zabe da wuraren da aka kai su, tare da daukar alkawarin cewa duk lokacin da hukumar za ta yi wani taro na masu ruwa da tsaki kungiyar na cikin sahun gaba saboda muhimmanci da irin tsare-tsaren da suke da shi.

Tunda da farko da yake nasa jawabin a kan makasudin wannan ziyara ta su, shugaban tafiyar kuma daya daga cikin kwamitin amintattu na kungiyar, Farfesa Abdulaziz Ahmad Mashi, ya bayyana cewa tuni suka so kawo ziyara amma yanzu Allah baya kaddara hakan.

Ya kara da cewa suna son hada gwuiwa da hukumar zabe domin ba da ta su gudunmawar wajen ganin jama’a sun yanki katin zabe kuma kungiyarsu ba ta da alaka ta nesa ko ta kusa da kowace irin jam’iyyar siyasa.

Farfesa Mashi, ya ce bisa haka ne suke neman cikakken bayani game da ayyukan wannan hukuma wanda hakan zai ba su damar sanin ta inda za su ba da gudunmawa ganin cewa mafi yawansu a tafiyar matasa ne.

Sannan ya nemi hukumar zabe da ta dauki kungiyar a matsayin abokiyar tafiya wajen isar da sako ga al’ummar Musulmi ba wai sai ‘yan darika kawai ba.

A nasa ta’alikin sakataren tsare -tsaren kungiyar, Awwal Abba Yahaya, ya ba da tarihin kafuwar kungiyar da kuma dalilin da ya sa aka kafa ta tare da yin bayanin irin tsarin shugabancin da suke da shi a matakin jiha da shiyya da kananan hukumomi zuwa mazabu.

Abba ya ce suna amfani da hanya mafi sauki wajen isar da kowane irin sako ake son isarwa ga mambobinsu, ko dai ta hanyar haduwa a Masallatai na yau da kullum ko kuma duk sati wajen zikirin Juma’a.

“Kimanin shekaru bakwai ke nan da kafa wannan kungiya wanda take da wakilin kowane bangare a darika kuma muna da shugabanni tun daga matakin jiha da shiyya da kuma kananan hukumomi, har da matakin rumfa, kuma babu ruwanmu da wata jam’iyyar siyasa, muna yin wanna tafiya ne ganin yadda aka bar mu a baya akan batun siyasa amma yanzu mun farka kuma za a damu da mu” inji shi

Daga karshe sakataran tsare-tsaren, ya ce sun shirya tsaf domin ci gaba da wayar da jama’a a kan wannan hidima ta katin zabe, inda ya ce za su yi amfani da kafafen yada labarai wajen isar da sakon, tare da ba da tabbacin za a ga canji nan kusa ba nesa ba.

INEC
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

Hamshakin Dillalin Kwayoyi Ya Shiga Hannu A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.