• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Yadda Aka Siyasantar Da Cutar Covid-19 Ya Fi Cutar Barna

by CMG Hausa
3 years ago
COVID-19

Kwanan baya, kasar Amurka ta sanar da daukar matakan kayyade shigar baki kasar daga kasar Sin, bisa dalilin da ta bayar na wai “yaduwar cutar a kasar Sin ka iya haifar da sauye-sauyen fasalin cutar”. Amma, ko da gaske ne Amurka ta dauki matakin ne don magance cutar?

A hakika, nau’o’in cutar Covid-19 da yanzu haka ke yaduwa a kasar ta Sin, tuni sun yadu a Amurka da ma sauran wasu kasashen duniya kafin a gano su a kasar Sin. Misali, cutar nau’in BA.5 da ke yaduwa a kasar Sin ta kasance wadda aka fi fuskanta a kasar Amurka a watannin da suka gabata, baya ga cutar nau’in XBB.1.5 da kwanan baya aka gano ta a biranen Shanghai da Hangzhou na gabashin kasar, daidai ta kasance cutar da a halin yanzu taka fi yaduwa a kasar Amurka. A sa’i daya kuma, a yayin da cutar ke yaduwa a fadin duniya, sauye-sauyen fasalin cutar ka iya faruwa ko ina a duniya. Don haka, masana ilmin cututtuka masu yaduwa na kasashe da dama, sun bayyana ra’ayoyinsu na rashin yarda da daukar matakan kayyade shigar baki daga kasar Sin, baya ga kuma wasu hukumomin lafiya da suka hada da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Turai suka bayyana cewa, bai dace ba a kayyade shigar baki daga kasar Sin.

Da haka muke ganin cewa, kasar Amurka na daukar matakin ne don siyasantar da cutar.

In mun waiwayi shekaru uku da suka wuce, za mu ga cewa, gwamnatin kasar Amurka ba ta taba mai da hankalinta a kan daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta ta fannin kadagarkin cutar ba, a maimakon haka ma, tana ta kokarin siyasantar da cutar ne, lamarin da ya sa wannan kasar da ke sahun gaba a duniya ta fannin harkokin kiwon lafiya, ta gamu da munanan hasarorin da bai kamata ba, inda ‘yan kasar sama da miliyan 100 suka harbu da cutar, a yayin da sama da mutanen kasar miliyan 1.08 cutar ta halaka, baya ga kuma yara dubu 250 da suka zama marayu a sakamakon cutar.

Sabanin matakin da Amurka din ta dauka, hukumomin yawon shakatawa, da ofisoshin jakadanci na kasashe da dama da ke kasar Sin a kwanan baya, sun yi maraba da bakin kasar Sin zuwa kasashen su, don fatan ganin babbar kasuwar kasar ta taimaka ga farfado da tattalin arzikinsu, suna kuma fatan hada karfi da karfe tsakanin kasa da kasa, zai fitar da duniya daga mawuyacin halin da ake ciki. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Next Post
Matsalar Bazuwar Fyade Zuwa Kan Kananan Yara Maza

Matsalar Bazuwar Fyade Zuwa Kan Kananan Yara Maza

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.